28/06/2026
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya kai ziyara ga iyalan marigayiya Ummulkhairi, matashiyar da aka kona a yankin Maraban Jos a makon da ya gabata.
A yayin ziyarar, gwamnan ya jajanta wa iyalan mamaciyar tare da bayyana alhininsa kan wannan mummunan lamari da ya girgiza al'umma. Ya tabbatar musu cewa gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an yi cikakken bincike tare da hukunta duk wanda aka samu da hannu a wannan aika-aika.
Gwamna Uba Sani ya kuma bayyana cewa jami'an tsaro sun k**a mutane 41 da ake zargi da hannu a kisan, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike domin tabbatar da adalci. Ya yi kira ga al'umma da su kwantar da hankalinsu, su guji daukar doka a hannunsu, tare da bai wa hukumomin tsaro hadin kai domin tabbatar da zaman lafiya.