UMMU Aïsha's Library

UMMU Aïsha's Library Novels only

09/09/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE 🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 69/70

___________Ahankali nanny ta fara magana ,tana cewa"Ammi ba ita bace asalin mahaifiyar Adeeb,amma itace wacce ta rikeshi bayan ta kashe mahaifiyarsa."

Dararrararaammm!!!gaban fattu ya bada ƙara, sak**akon jin maganar nanny datayi k**ar saukar aradu,
Da sauri ta dafe gefen kujerar da take kai,dan ji tayi k**ar zata faɗi.
Baki buɗe take kallon nanny cike da tsantsar mamaki,cikin rawar murya tace "nanny kina nufin ammi itace ta kashewa Hamma mahaifiyarsa?to amma me yasa Hamma yake mata kallon uwa?me yasa bai dauki mataki akanta ba?"fattu ta faɗa cikin rudani.

Ajiyar zuciya nanny tayi kafin tace "saboda bashi da masaniya akan abinda ya faru,kuma ya yarda da ammi fiye da kowa,dan yana mata kallon uwa mahaifiyane,baya tunanin zata taba cutar dashi.ki saurare Ni da kunnen basira ,zaki ji abinda ya faru yanzun nan.

"Sarauniya Nazli,ƴace agurin ƙarin baban mai martaba uwa daya uba daya,wato kenan ita da mai martaba ,yan uwan juna ne ,dan kuwa auren zumunci akayi musu.
Suna kaunar juna matuka bayan anyi auren,suna zamansu lafiya cikin so da aminci, lokacin da akayi auren nasu,iyayen sarauniya Nazli duk sun rasu,hakan yasa take zaune a hannun mahaifiyar mai martaba ,dalilin hankali da nutsuwarta yasa mahaifiyar mai martaba ta zaba masa ita matsayin matar da zai aura inda ranar da aka daura musu aure aka naɗa shi matsayin sarkin misra.

Shekara guda dayin aurensu Allah ya azurtata da zamu yaro , kyakykyawa abin so ga kowa, ranar suna aka rada masa suna adeeb.

Adeeb ya taso cikin so da kauna, agurin iyayensa, da ma duk wani wanda yake fadar nan,yana da matukar hakuri ,hazaka ,ladabi da kuma biyayya.
Nice wacce ke rainon Adeeb ,kasancewar mijina yana aiki acikin fadar nan,shine drivern dake tuka sarki da iyalinsa.
Lokacin ina goyon dana tareeƙ ,dan haka na hadasu duka ina rainonsu,saidai ko da wasa ban taba hada tareeƙ da Adeeb matsayi daya ba,duk l

09/09/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 65/66

________________"Ki sanar dani dalilin da yasa baki son zuwana gurin yarinyar nan?
Me alaƙarki da ita ?ko ince me ta tsaremiki uktee?
Sarauniya suhaimat ta fada cikin haɗe fuska ,dan tasan kadan daga aikin ammi ta hanata zuwa gurin fattu.

Zaro ido ammi tayi tana mai kallon suhaimat ,dan sai lokacin ta fahimci tana kokarin bada kanta,cikin in-ina ta fara magana "su...hai..mat,wane dalilin ne zaisa kuwa in hanaki zuwa gurinta?kawai ina gudun ace ko wata munaƙisar muka ƙulla yasa k**e ta zarya,kinsan tunda wannan abun ya faru to komai ma laifi zai zama , amma bayan wannan bani da wani dalili"ammi ta fada tana kafe suhaimat da idanu.

Murmushi suhaimat tayi ,kafin tace "Indai dan wannan ne karki damu ,ai kowa yasan Ni likitar matace,kuma ba laifi bane idan naje duba marar lafiya,kuma ma mace"suhaimat ta fada cikin yanayi na rashin damuwa.kafin ta juya ta bar ɗakin.

Harara ammi ta biya da ita ,k**ar idanunta zasu fado ,haushin suhaimat takeji fiye da tunanin mai tunani,wllh badan tana tsoron faruwar wani abu ba ,data gama da suhaimat ,dan itace silar shigar ta ko wace irin damuwa.amma ba komai muje zuwa sannu sannu bata hana zuwa,saidai dade ba'ajeba.

koda sarauniya suhaimat ta koma bangaren Adeeb, kwance ta tarar da fattu adaki, idanunta alumshe k**ar mai barci,yayinda Adeeb ke falo yana amsa waya.
Bayan sun gaisa yake sanar da ita fattun tana cikin daki, dan sosai yake jin dadin yadda take kula masa da fattu.

Tana shiga fattu ta buɗe idonta,da sauri sak**akon jin muryarta,dan dama tana kwancen nan, tunaninta Sarauniya suhaimat kawai take.
Da murna ta tashi zaune tana murmushi,tare da kallon suhaimat,

Itama cikin farin ciki ta karasa gareta ta zauna.
Ahankali fattu tace "inna nayi tunanin bazaki dawoba,ina ta tunaninki araina"ta fada fuskarta ɗauke da annuri.

Shafa fuskar fattu tayi kafin tace "ƴata kenan ,tunda nace zan dawo ,ai dole na

09/09/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 63/64

_______________Jikin nanny ne yayi sanyi sosai,ganin Adeeb atsaye,kuma ya gansu tare da amma,tasan yanzu kam kome zata faɗa masa ,bazai taba yarda da ita ba.ahankali take takawa zuwa gareshi,gaba ɗaya jikinta ba kwari,
Shikuwa Adeeb yana tsaye ya kafeta da Mayun idanunsa ,masu sanya mutum yaji shi cikin tsoro da fargaba.
Nanny Tana karasowa tace "magajin fada ,fushi kake dani ko"?
Ta fada cikin sanyi murya da mutuwar jiki.

Lumshe ido Adeeb yayi ,zuciyarsa na masa zafi yana mamakin abinda nanny tayi masa,ace wai nanny ta hada kai da maƙiyarsa tana tayata ƙoƙarin cutar dashi,matar daya ɗauka matsayin uwa ?mutum kenan.
"Ko kaɗan nanny bana fushi dake,kawai ina godiya ga Allah ne ,daya nunamin gaskiya ,na gane irin mutanen da nake tare dasu,na daukeki tamkar mahaifiyata nanny,Amma bansan nayi babban kuskuren yin hakan ba,dan Allah kiyi haƙuri"ya faɗa yana mai haɗe hannayensa guri ɗaya alamun neman afuwa.

Sosai nanny kejin ciwo cikin ranta ,damuwa da taraddadi sun cika mata zuciya,dama tayi wannan tunanin,tasan idan har Adeeb ya gansu tare da amma ,to shikenan,kuma kome zata faɗa masa bazai yarda da ita ba,amma Allah shine shaida bata da nufin cutar da Adeeb ko kaɗan.

"Magajin fada wllh abinda kake zargi ba haka bane ,kada ganina tare da amma yasa maka kokwanto akaina, wllh nima Ina jinka tamkar tareeƙ bazan taɓa cutar dakaiba magajin fada.
Nanny ta faɗa cike da damuwa aranta.
Girgiza kai kawai Adeeb yayi tare da barin gurin,zuciyarsa k**ar zata fashe tsabar damuwa .
Kallonsa kawai nanny keyi,tana fatan Allah yasa ya gane gaskiya cikin sauri kafin komai ya daɗa lalacewa.

Ba kowa cikin falon ammi,sai ƙamshi dake tashi ta ko'ina ,dan ammi akwai son kamshi,kai tsaye ya nufi dakin kwananta, nocking yayi amma shiru,hakan yasa shi shiga cikin dakin kai tsaye.saidai nan ma ba kowa cikin dakin.

Harya juya zai fice ,sai kuma zuciyarsa ta raya masa

09/09/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

page 61/62

________________Ficewa s**ayi daga part ɗin ammi zuwa na Adeeb, haka kawai gaban sarauniya Nazli ke faduwa,sam ta kasa gane kan wannan faɗuwar gaban nata,saidai kawai ta alaƙa ta hakan da tunanin halin da zata ga yarinyar data sanya tausayi ta cikin zuciyarta.

Su zayyad ma biyo ta s**ayi,dan sunce suma son gannin marar lafiyar ,kuma zasuyi wasa agurin uncle Adeeb ɗin.

Suna zuwa Adeeb ya dannan lambobin securityn daya sanya lokacin da zai fice,nan take ƙofar ta bude s**a shiga.
"Tana cikin daki" Adeeb ya faɗa yana kallon sarauniya suhaimat wacce ke tsaye cikin faduwar gaba.
Kallonsa tayi cikin tausayawa, tare da jinjina kai .

sam zuciyarsa Adeeb da jikinsa basa masa daɗi, yana cikin matsananciyar damuwa ,abubuwa sunyi masa yawan da har yana rasa me Yak**ata yayi.

" Ku zauna anan maza kafin na fito kunji" ta faɗa tana shafa kan yaran nata,kafin tabi bayan Adeeb zuwa cikin dakin.
Tana kwance k**ar yadda ya barta,ruwan daya ɗaura mata ya kusan karewa.
Jiki asanyaye sarauniya suhaimat ta karasa bakin gadon da fattu ke kwance .sosai bugun zuciyar sarauniya suhaimat ya tsananta.
Zama tayi tare da ƙurawa fattu idanu,lokaci guda taji wata masifaffiyar kaunar yarinyar tana ratsa dukkan sannan jikinta,ji take k**ar bata taɓa son abu mak**ancin yadda take jin son yarinyar na shiga lungu da sako na jikinta ba.

Hannun fattu ta kamo tare da riƙewa gam-gam cikin nata,wani sanyi taji yana ratsata lokacin data k**a hannun fattun,batare da saninta ba kawai ta rungume hannun fattu aƙirjinta ,tare da runtse idonta.wani irin shauƙi takeji yana shiga jikinta irin na ƙaunar dake tsakanin ɗa da uwa.haƙika takamu da matsananciyar kaunar yarinyar lokaci guda.

Kallon fuskar fattu take bata ko ƙifta idanunta,Adeeb na tsaye agefe guda yana kallonta ,mamakin yadda yaga fuskarta ta nuna so da kaunar fattu yake,koda yake haka Allah ke al'amarinsa.ganin ta kasa cew

09/09/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE 🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 59/60

________________Ahankali nanny ta ke kallon Adeeb,kafin ta sauke ajiyar zuciya,tunani take ta yadda Adeeb zai karbi wannan magana,ta yaya zata sanar dashi cewar,amminsa itace silar faruwar komai?shin zai amince da abinda zata faɗa masa ko yaya? Wane irin kallo zai musu idan yasan cewa amminsa ce ta kashe sarauniya Nazli da yaranta tare da baban tareeƙ,kuma abakinsu?anya kuwa basu barowa kansu aiki ba?
"Nanny kiyi magana mana kinyi shiru, ki sanar dani wake da hannu akan hadarin nan?"

Da sauri nanny ta dawo daga dogon tunanin data tafi,kallon tareeƙ tayi cike da karayar zuciya ,amma cikin ƙarfafa gwuiwa tareeƙ ya kalli nanny yana mai jinjina kai da nuna alamun ,kwantar da hankali.
Ajiyar zuciya nanny ta sauƙe Tana mai kallon fuskar Adeeb,kafin ta fara magana.
"Magajin fada k**ar yadda na faɗa maka,wasu abubuwan muna kallonsu ne ba a yadda suke ba,ka sani abinda zan faɗa maka ba ƙarya ,ba kuma cutarwa.shiru ta ɗanyi tana jinjina maganar kafin taci gaba"ba kowa ya shirya wannan hadarin ba, face Amminka"nanny ta faɗa tana mai kure Adeeb da ido.

Da wani irin slow Adeeb ya mike tsaye bakinsa bude,zuciyarsa na wani irin bugawa k**ar guduma, ji yayi kunnensa ya ɗauki wani ƙara ƙuuuuuuuu!!!
Sai yake jin maganar ta nanny Tana rarrabewa,k**ar baiji me take faɗi daidai ba,jikinsa rawa ya k**a,ta yadda yana mikewa tsayen yaji k**ar zai fadi dan haka da sauri ya koma ya zauna,idanunsa ƙuri,akan fuskar nanny,
Cikin in-ina ya ke cewa"na...nan.,...y mek....Ike ..son....f..a...ɗ..I n..ee." ya faɗa numfashinsa na rarrabewa,ji yake k**ar zuciyarsa zata fito tsabar yadda take bugawa.

Da sauri nanny ta ƙaraso kusa da Adeeb ta zauna ,cikin nutsuwa take shafa bayansa tare da kallon fuskarsa cikin tausayawa,dole yaji maganar tazo masa k**ar saukar aradu."ka nutsu Adeeb domin Abinda nake faɗa maka yana buƙatar nutsuwa,tabbas Amminka itace ta shirya wannan hadari,t

09/09/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE 🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 57/58

________________Gimbiya suhaimat ta gama tsara cewa data huta zataje part ɗin Adeeb dan ganin yarinyar nan,
Saidai shigarta part ɗin ammi da yanayin da taga ammin yasa ta saurin,ƙarasawa cikin dakin ,cikin damuwa take faɗin"ukktee meke damunki? Yana ganki akwance?gimbiya suhaimat ta faɗa tana kamo hannun ammi ,wanda ba'a daura mata ruwa ajikinsa ba.

Ahankali ammi wacce tayi nisa cikin tunani ta buɗe idonta tana kallon gimbiya suhaimat,kafin ta sauke ajiyar zuciya tare da lumshe ido ta buɗe" ke dai bari suhaimat,yau naga abinda ban taba gani ba arayuwata,nan ta bata labarin abinda ya faru,saidai ta boye mata asalin labarin fattu,sai cewa tayi wata baiwa ce Rashad ɗin yayiwa fyade,dan ita atunanninta Rashad yayiwa fattu fyaɗen.

Sosai gimbiya suhaimat ta tausayawa yarinyar,sannan tayi Allah wadai da halin Rashad,zuciyarta na tsananin bugawa ,har cikin ranta take jin tausayin yarinya.kuma tayi alwashin ,saitaje taga yarinyar nan kafin ta bar ƙasar.

Rashad kuwa kai tsaye aka wuce dashi,lafiyayyen asibitin dake masarautar,emergency akayi dashi,cikin gaggawa likitoci s**a duƙufa akansa dan ceto rayuwarsa.
Dan da dama cikin likitocin , sunyi tunanin hatsari ya samu mai muni.
Karon farko ruwa s**a fara ɗauka masa,kafin s**a fara bincikarsa,karayama kusan biyar ce ajikinsa, bayan munanan raunuka dake jikin sa,sannan since kansa ya bugu ,dole sai sunyi bincike akwakwalwarsa, dan tabbatar da lafiyarta.

Amma kuka take sosai cike da tarin damuwa da baƙin ciki ,meyasa Rashad zaiyi mata haka?me yasa gaba ɗaya halayyar Rashad ta sauya ne?da ɗan ta mai hankaline da nutsuwa ,sannan yana bin maganarta,amma daga baya ya fandare ya zama gagararre,yanzu ga irin abinda ya jama kansa.karaya har biyar ajikin mutum.Nan dai taci kukanta ta ƙoshi,tana zaune gefen ɗan ta.

Nanny ma ta farfaɗo ,hankalinta amatukar tashe ,tana zaune hawaye na zuba cikin idanunta,yayin

09/09/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE 🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 55/56

_________________"RASHAAADDDD"
Aka kwallah kiran sunan Rashad,Wanda saida ɗakin ya amsa.gaba dayan mutanen da s**a shigo ɗakin saida s**a tsorata ,saboda yadda amon Muryar ya fito da mugun ƙarfi da sauti mai firgitarwa.

Ahankali fattu da ke neman macewa ta buɗe kunburarrun idanunta da gyar,ta saukesu akan fuskar hammanta, wata shashshekar kukace ta zo mata ,numfashinta na hawa da sauƙa ,da gyar ta daga hannunta tana mikawa Adeeb ,

Da wani irin mugun sauri Adeeb yayi kanta yana mika mata nashi hannu,saidai kafin ya ƙara so tuni hannun nata ya koma ƙasa sharaff!! Ahankali kuma idanunta s**a kulle ,duk wata jijiya dake jikinta tasaki,ataƙaice dai fattu ta sume.
Wani irin ƙara Adeeb ya kwalla mai matukar firgitarwa ,hayaƙi na fita ta bakinsa da hancinsa, hannun fattu ya k**a ya riƙe cikin nashi tare da damkewa k**ar zai balla hannun nata.
Jikinsa gaba ɗaya rawa yake k**ar ana kaɗa masa gangi,ɗago da kansa yayi afusace ya sauke idanunsa akan Rashad,Wanda tsabar tsoro ya kasa koda matsawa daga kan table ɗin gashi tsirara haihuwar uwarsa.
Da sauri Rashad ya runtse idanunsa,numfashinsa na wani irin hawa da sauka k**ar shima zai shide tsabar tsoron ganin yadda idanun Adeeb ya koma,ga wani irin bakin hayaƙi daya fara cika ɗakin,
Wani ƙaran Adeeb ya sake kwalla,wanda yafi na farko sanya tsoro da razani,gaba ɗaya dakin yayi wani irin bakiƙirin ,baka ko ganin hannunka bare na kusa dakai.

Su ammi da amma,nanny tareeƙ ,jakadiya,da Zulaihat wacce zuwan ta kenan,bangaren dan ta sami labari gurin yan s.i.d ɗinta.gaba daya tsoro ,firgici da tsantsar mamakin abinda ke faruwa yasa sun kasa koda motsine agurin ,bare suyi wani abu.
Sun ƙanƙame juna jikinsu yana wani irin bari,nanny Banda sunan Allah ba abinda take ambata"innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, meye wannan ke shirin faruwa haka,tareeƙ kana ina bana ganin komai fa " nanny ta faɗa tana ƙanƙame tar

09/09/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 53/54

________________Gaba ɗaya Rashad ya zama k**ar wani mahaukaci,ba abinda ke gabansa face biyan buƙatarsa.
Gaban rigar fattu ya k**a da karfin tsiya ya tsargeta ,tun daga sama har ƙasa.

Nan da nan farar best ɗin fattu da baƙin skin tite ɗin ta s**a bayya, Allah ma yasa wandon har ƙasa yake.
" Wllh yau ko da zaki mutu ,saina ida nufina akanki,banga wanda zai iya karbarki daga hannuna ba" Rashad ya faɗa cikin wata irin murya ta azzalumai,waɗanda s**a manta da cewar Allah yana kallonsu duk abinda suke aikatawa.
Da gyar fattu ta iya buɗe rinannun idanunta ,wanda tsabar mari da kuka s**a sanya idanun kumbura sosai.
Ahankali take daga lips ɗin ta magana take amma saiƙa kura mata ido zaka fahimci me take cewa."wallahu galibun ala amrina" shine abinda take ta maimaitawa abakinta.
Ƙoƙarin zare skin tite ɗin Rashad keyi amma sam ya kasa,jikinsa sai rawa yake,yana jin k**ar wanda ake jona masa shocking,Amma tsabar masifa da jaraba ,yaki fasa abinda yakeyi,
Cikin haushi,ya ƙara kaiwa kumatun fattu mari mai zafi da shiga jiki."Dan ubanki me kikasa ajikinki?idan na taɓaki nakejin k**ar ana zuƙemin jini?"Rashad ya faɗa yana mai kai fuskarsa saitin Tata,bakinsa ya ɗora akan na fattu,aikuwa ba wata wata fattu ta gartsa masa cizo alips ɗinsa.kara ya kwalla yana mai komawa gefe dafe da lips ɗin sa na ƙasa "kai -kai -kai Ni kika ciza Dan uwarki?zaki gane kurenki ,wllh yau saina kusan kasheki Shegiyar yarinya mai taurin kai"Rashad ya faɗa yana mai danƙo gashin fattu ,wanda yayi buju-buju.

Fattu fa ko motsin kirki bata iyayi,gaba ɗaya jikinta ya saki,tunda take a rayuwarta,bata taɓa shiga tashin hankali da azaba irin na yauba.
Sunan Allah kawai take ambata cikin ranta.

Adeeb kuwa cikin gaggawa yayi jawabinsa tare da godiya ga baƙin da s**a zo dan tayashi murnar dawowa gida cikin ƙoshin lafiya.sosai ƙirjinsa ke mugun bugawa zuciyarsa k**ar zata fito waje,id

09/09/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 51/53

_________________Abakin ƙofar hall ɗin Zulaihat ta tarar da Rashad ,yana tsaye da waya ahannunsa ,da alama kira yake ƙoƙarin yi,saidai yana ganinta ya maida wayar cikin aljihunsa yana mai faɗin,"yawwa dama ke nake ƙoƙarin kira,sai gaki kin fito.

Ƙarasowa Zulaihat tayi kusa dashi ta tsaya" ya ake ciki ne ?" Ta faɗa tana ɗan waigen bayanta.
"Yau burina zai cika ,zan sami abinda ke hanani barci,kuma zanyiwa Adeeb illah,saina rama dukan da yayi min akan yarinyar da yake iƙirarin yar amanar da ce,bayan kuma Ni nasan dadironsa ce ,kawai kishine da mugunta s**ayi masa yawa,shine ya hanani Nima in ɗana"cewar Rashad yana mai kallon Zulaihat.

"Kaga Rashad karka ƙara cewa dadiron my Prince ce,karkayi masa sharri,dan kuwa nasan halinsa nasan koshi waye,wllh bazai taba ajiye yarinyar nan dan biyan buƙatarsa ba,mutumin da har maganin sha'awa nake saka masa alemo,dan kawai yayi tarayya dani,amma duk yadda ya galabaita bazai koda rungumeni ba.
Dama dai kaine akace ka ajiye ta dan biyan buƙatarka,to wannan kam na yarda dan nasan kai din namamajo ne " Zulaihat ta faɗa tana mai galla masa harara,dan taji haushin sharrin da yayiwa adeeb,ita da take burin ace itace zata fara bude Adeeb aledarsa ina zataso jin wannan batu.
Wani shegen kallo Rashad ya watsa mata kafin yace " banza yar tasha ,ke har Ni zaki cewa na mamajo? Ai duk iskancina ban kaki ba,kefa ƴar maye ce sannan jarababbiya, Ni kaina sau nawa ina taimaka miki ?ina ce wataran har guduwa nake saboda jarabarki ?zaki raina min hankali wawiya kawai" Rashad ya faɗa cikin faɗa.

Haushi sosai ya k**a Zulaihat ,ranta ya ɓaci da kalaman Rashad gareta ,wato har gori zaiyi mata ,dan ta neme shi kusan sau uku ?ba komai zai gane kurensa wllh.
"Ni kakeyiwa gori Rashad ?to wllh kasani bazan taimaka maka akan ƙudirinka na yauba ,saidai kayi kai kadai ,banza marar mutunci" Zulaihat ta faɗa cikin ɓaci rai tana mai ba

09/09/2022

MACIJI NE🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 49/50

_______________Tashi Adeeb yayi cikin nutsuwa, da takunsa irin na jaruman maza ,ya nufi ɗakin da fattu ke ciki.

Fattu na zaune abakin gado, tayi shiru k**ar mai tunanin wani abu,Adeeb ya turo ƙofar da sallama ɗauke abakinsa,saidai idan ba ka kasa kunne ba ,to bazakaji me yake faɗi ba.

D**o Kai fattu tayi jin muryar Adeeb datayi,baki buɗe take kallon Adeeb ,tunda take arayuwarta,zata iya cewa bata taɓa ganin mutum mai kyau irin na Adeeb ba ."masha Allah"fattu ta faɗa tana mai mikewa tsaye fuskarta ɗauke da murmushi,ta ƙure Adeeb da ido k**ar yau ta taɓa ganinsa.

Ƙarasowa Adeeb yayi cikin ɗakin,shima idonsa na kanta ,dan haka kawai yaga tayi masa kyau shima .
Ɗan harararta yayi kafin yace " Please karki cinyeni da kallo mana"ya faɗa yana ɗan wani gwabe fuska cikin shagwabar da baisan yayi ba.

Da sauri fattu ta sanya hannu tare da rufe fuskarta tana ɗan dariya ,dan kunya taji da yadda yayi salon maganar tasa.
"Hamma kayi kyau sosai ,kai mai kyaune" fattu ta faɗa kanta a ƙasa tana ɗan mirza hannunta.

Wani irin sanyi ne yake ratsa zuciyar Adeeb, sosai yaji daɗin maganar fattu ,dan haka cikin wani irin shauƙi ya mika hannunsa tare da d**o habarta .kallon juna suke ido cikin ido,murmushi Adeeb yayi kafin yace "kin tabbata nayi kyau a idonki?wankana yayi miki kyau?" Ya faɗa yana mai kallon lips ɗin fattu ,wanda yake ji k**ar ya cinyesu.

Lumshe ido fattu tayi tare da jinjina kai tace " Hamma bantaɓa ganin mutum mai kyan ka ba,kuma Ni kullum ma kyau kakemin" ta faɗa tana ɗan riƙe lips ɗin ta na ƙasa da haƙoranta.

Wani irin abu Adeeb yaji yana masa yawo ajikinsa,sosai yake jin yana son rungumar fattu ajikinsa ,duk lokacin da yake tare da ita yakan tsinci kansa cikin wani irin shauƙin son kasancewa da ita .

Murmushi yayi tare da shafa gefen fuskarta yace " to me zaki bani matsayin kyautar dazan fita gurin taro da ita?" Ya faɗa idanunsa akan lips ɗin ta.

Shiru f

02/08/2022

🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄

MACIJI NE💘💘

Na mammy kabeer
(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book

Page 45/46

________________kai tsaye Adeeb part ɗin sa ya wuce da fattu ,wacce ke kuka k**ar ba gobe ,gaba ɗaya atsorace take da ganin yanayin na adeeb.ita tsoronta ma kada wani abu yasameshi, ko ya sanja halitta .

Suna shiga Adeeb ya zaunar da fattu akan kujera ,sam baidamu da yadda jikinta ya ɓaci ba,wani irin tuƙuƙin baƙin ciki yake ji cikin zuciyarsa ,lallai Rashad ya taɓowa kansa ,inhar ya ce zai nuna halin ɗan akuyancinsa akan fattu,to zai iya aikata masa komai ma,dan bazai taɓa iya daukar kowane irin abu akan fattu ba,duk ƙanƙantarsa kuwa.

Kaiwa yake da kawowa atsakiyar ƙarin falon kashi,banda dukan hannunsa ba abinda yake ,idanunsa sunyi bala'in sauyawa ,wannan karon gaba ɗaya idon nashi sun koma blue sosai ,sai wani irin huci yake k**ar zaki.

Fattu kuwa ta takure guri ɗaya ,atsorace take sosai,ta kasa koda kallon Adeeb ne ,dan gaba ɗaya k**anninsa sun sauya,har wani bari jikinsa keyi.
Kuka take ƙasa ƙasa ,yayi da take jin yadda jini ke zuba ajikinta,dan har zuwa lokacin akiɗime take.

Juyowa Adeeb yayi yana kallon fattu ,tausayi ta yake ji sosai cikin ransa,yana tuna cewa itaɗin amanace agurinsa,dole ya kula da rayuwarta,bayan haka yana jin tamkar ita ɗin rayuwarsa ce ,bazai bari wani abu ya cutar da ita ba.

Gurin ta ya nufa cikin takunsa mai cike da izza,tsugunnawa yayi agabanta tare da tsura mata ido,d**owa tayi da sauri itama tana kallonsa.da sauri ta sunkuyar da kanta tana kuka ." Dan Allah Hamma kayi haƙuri,kada wani abu ya sameka " ta faɗa tana mai d**owa tare da kallon cikin idanunsa.

Shima kallonta yake cike da tausayawa,hannunsa ya ɗora akan fuskar fattu yana mai share mata hawaye,idanunsa akan fuskarta,
Ɗayan hannun nashi yasa tare da riƙe duka kumatunta,yana kallonta,tsawon mintuna yayi yana kallonta ,kafin ya sauƙe ajiyar zuciya da ƙarfi kafin ya fara magana ,cikin ƙunar zuciya .

" Hulwa " ya faɗa ahankali yana mai kallon f

Adresse

Zinder

Site Web

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque UMMU Aïsha's Library publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager