15/04/2026
Farin jini daga Allah! Kungiyoyin Mata Sun Nuna Goyon Baya ga Sadaukin Jibia
Kungiyoyin mata guda biyar daga gundumomi 11 na karamar hukumar Jibia a jihar Katsina sun gudanar da taron nuna goyon baya ga Hon. Muhammadu Halliru (Sadaukin Jibia kuma Sardaunan Kaita), mai neman takarar kujerar majalisar wakilan Najeriya domin wakiltar kananan hukumomin Kaita da Jibia a zaben 2027.
Jaridar ta ruwaito cewa, taron ya gudana a ranar Laraba, 15 ga watan Afrilu, 2026 a garin Jibia, inda matan s**a bayyana bukatar su ga Muhammadu Halliru ya amsa kiran al’umma domin ceto yankin daga abin da s**a kira “wakilci marar amfani” daga dan majalisar mai ci a yanzu, wanda s**a ce bai kawo wani ci gaba mai ma’ana ba.
A jawabinta, Hajiya Hadiza Musa Mota ta nuna farin cikinta da yadda mata s**a halarci taron, tana mai kira ga Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, da ya tsayar musu da Sadaukin Jibia a matsayin dan takara. Ta ce tun kafin ya samu kujera, Sadaukin Jibia na taimaka wa mata, matasa da kananan yara, ta bangaren tallafi da inganta rayuwa. Ta kuma koka da cewa wakilin da ke kan kujera yanzu ba ya kai ziyara ga al’ummar yankin domin jin halin da suke ciki.
Ita ma Hajiya Aisha wadda aka fi sani da Ɗiya, ta bayyana cewa matan yankin sun gaji da wakilcin da ake yi a yanzu, tana mai cewa suna bukatar Muhammadu Halliru saboda ayyukan alherin da yake yi, musamman taimakon marayu da mata, da kuma tallafawa asibitoci ciki har da samar da muhallin jinya ga mata. Ta ce a Jibia da kauyukanta, babu wanda bai san irin taimakon da yake bayarwa ba.
A nata bangaren, Hajiya Ansau, ta jaddada cewa matan yankin na alfahari da Sadaukin Jibia, saboda yadda yake taimakon al’umma ba tare da nuna wariya ba. Ta ce suna rokon Gwamna Radda da ya tsayar musu da shi domin ya wakilce su a majalisar wakilai, tana mai cewa hakan zai kawo sauyi mai kyau ga yankin.
Kungiyoyin matan sun sake jaddada rokon su ga Gwamnan jihar Katsina da ya bai wa Hon. Muhammadu Halliru tikitin takara, yayin da masu sharhi s**a bayyana cewa siyasar Kaita da Jibia na kara daukar sabon salo. Sun ce idan Hon Halliru ya samu damar tsayawa takara kuma ya yi nasara, ana sa ran zai kawo sauyi mai ma’ana a wakilcin majalisar wakilai ta hanyar mayar da hankali kan bukatun jama’a da ci gaban yankin.