Dan Takara

Dan Takara Aikin jarida ya kasu kashi-kashi da dama, kamar:
Jaridar bincike (Investigative journalism): inda ake zurfafa bincike kan wani lamari.

Jaridar rahoto (News reporting): watsa labarai kai tsaye. Jaridar ra’ayi (Editorial/Opinion): bayyana ra’ayin marubuci

20/05/2026
20/05/2026

SUBHANALLAHI: Yanzu Wata babbar motar ɗaukar kaya Trailer ta yi mummunan hatsari a yankin Mile 3 Sabuwa da ke cikin garin Gombe, inda ta shiga cikin wasu shaguna dake titin da mutanen dake wajen tare da haddasa asarar dukiyoyi masu yawa.

20/05/2026

Haj. Zainab Baban-Takko, wadda take neman takarar Majalisar Dokokin Jihar Bauchi a mazabar Bauchi ta Tsakiya ƙarƙashin Jam'iyyar APC, ta sanar da janyewa daga zaben fidda gwani. Ta ce ta ɗauki matakin ne bayan nazari da lura da yadda tsarin yake gudana, inda ta bayyana rashin gamsuwa da bin ƙa’idojin dimokuraɗiyya.

Ta ƙara da cewa janyewarta ba fushi ba ne ko rashin nasara, illa dai mataki ne na ƙa’ida da ta ɗauka cikin nutsuwa da imani da gaskiya.

Ta gode wa magoya bayanta da s**a mara mata baya, tare da kira gare su da su ci gaba da zaman lafiya da mutunta juna.

A ƙarshe, ta jaddada cewa za ta ci gaba da hidimtawa al’umma tare da addu’ar Allah Ya tabbatar da adalci da ingantaccen tsarin dimokuraɗiyya.

20/05/2026

DA DUMI-DUMI: Senator Shehu Buba Umar Ya Janye Daga Takarar Gwamnan Bauchi a Jam'iyyar APC

Sanatan Bauchi ta Kudu, Sanata Shehu Buba Umar, ya sanar da janyewarsa daga takarar gwamnan Jihar Bauchi a ƙarƙashin jam’iyyar APC gabanin zaɓen fidda gwani da aka shirya gudanarwa ranar 21 ga Mayu, 2026

A cikin wata sanarwa da ofishinsa ya fitar, Sanatan ya bayyana cewa ya ɗauki wannan mataki ne domin nuna rashin amincewarsa da yadda ake tafiyar da harkokin jam’iyyar a jihar, musamman abin da ya kira karya kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999, dokar zaɓe ta 2026, kundin tsarin APC na 2022 da kuma ƙa’idojin jam’iyyar.

Sanarwar ta kuma ce tun kafin ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takara a ranar 19 ga Afrilu, 2026, jam’iyyar APC a Bauchi ta shiga rikicin shugabanci, musamman a wasu muhimman muƙamai na kwamitin gudanarwa na jihar kamar Sakataren Jiha da Sakataren Tsare-tsare.

Sanata Shehu Buba Umar ya ce ya janye daga takarar ne a matsayin zanga-zangar siyasa, yana mai nuna damuwa kan yadda rikice-rikicen cikin gida ke barazana ga haɗin kan jam’iyyar a Jihar Bauchi.

20/05/2026

Rikicin APC ya tsananta a Kaduna kan zaben fidda gwani

Rikicin cikin gida ya rincabe a jam’iyyar APCin jihar Kaduna, bayan da tsohon Kakakin Majalisar Dokokin jihar, Yusuf Ibrahim Zailani da tsohon Sanata Danjuma Laah tare da wasu masu neman takara s**a yi watsi da sakamakon zaben fidda gwani na 'yan majalisar dattawa na jam’iyyar.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito masu korafin sun ce babu wani sahihin zaben fidda gwani da aka gudanar a fadin jihar, lamarin da ya kara bayyana rabuwar kai da ke kara tsananta a cikin APC gabanin babban zaben shekarar 2027.

Me za ku ce?

20/05/2026

Tirka Tirka

Yan Takaran Yan Majilsun Jihar Bauchi a qananan hukumo mi biyu sunci xaben su na fidfa gwani tun kafin karfe goma na safe. Shin wasu Yan Majlisu ne?

Yanxu a siyasar bana a ko ina kake Dole ka kula da kafarka, karkaje Inda za'a  KWARFEKA😊😄😄
17/05/2026

Yanxu a siyasar bana a ko ina kake Dole ka kula da kafarka, karkaje Inda za'a KWARFEKA😊😄😄

Shirin rantsar da shugabanin Jamiyyar APC na jihar Bauchi....Daga Sakatariyar Jamiyyar APC na kasa dake birnin tarayya A...
27/03/2026

Shirin rantsar da shugabanin Jamiyyar APC na jihar Bauchi....
Daga Sakatariyar Jamiyyar APC na kasa dake birnin tarayya Abuja wajen taron rantsar da sabbin shugabanin Jamiyyar APC na jihar Bauchi.

Address

Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dan Takara posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share