12/06/2026
SAKON TAYA MURNA DA FATAN ALKHAIRI GA HIS EXCELLENCY MUHAMMAD ABDULLAHI ABUBAKAR (SAN) A BIKIN CIKAR DEMOKURAƊIYYA SHEKARU 27
A madadin mambobi da magoya bayan A-20 FOR MAKAMA BABBA 2027, muna miƙa saƙon taya murna da fatan alkhairi ga Muhammad Abdullahi Abubakar (SAN) bisa zagayowar cikar dimokuraɗiyya shekaru 27 a Nijeriya.
Wannan rana ta kasance abin tunawa ga irin gwagwarmayar da aka yi domin tabbatar da mulkin dimokuraɗiyya, adalci, da bai wa al’umma damar zaɓar shugabanninsu cikin ‘yanci. A irin wannan lokaci, ya dace a yaba wa shugabanni masu hangen nesa da s**a bayar da gudummawa wajen bunƙasa tsarin mulki da ci gaban al’umma.
His Excellency Muhammad Abdullahi Abubakar (SAN), wanda ya jagoranci Jihar Bauchi daga shekarar 2015 zuwa 2019, ya kasance ɗaya daga cikin fitattun jagororin da s**a bayar da tasu gudummawa wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya, bin doka da oda, da kuma gudanar da mulki bisa tsarin gaskiya da rikon amana.
A wannan muhimmin lokaci na cikar dimokuraɗiyya shekaru 27, muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ci gaba da ba shi lafiya, hikima, basira da ƙarfin guiwa domin ci gaba da hidimtawa al’ummar Bauchi da Nijeriya baki ɗaya. Haka kuma muna addu’ar Allah Ya albarkaci tafiyarsa ta siyasa da shugabanci, Ya sanya alkhairi da nasara a dukkan ayyukansa na al’umma.
Dimokuraɗiyya tana bunƙasa ne da shugabanni nagari, masu hangen nesa da kishin jama’a.
Allah Ya ƙara ɗaukaka Makama Babba, Ya sa gaba ta fi baya, Ya kuma ci gaba da kare Nijeriya da Jihar Bauchi.
Barka da Cikar Dimokuraɗiyya Shekaru 27!
Daga: A-20 FOR MAKAMA BABBA 2027
Muna Goyon Bayan Nagartaccen Jagoranci Domin Ci Gaban Bauchi.