15/05/2026
SANARWA TA MUSAMMAN
Assalamu Alaikum wa Rahmatullah.
Ni, Cmrd. Nasir Abdullahi Mai Gwandu, Aspirant of Birnin Kebbi North, tare da sauran abokan tafiyata, magoya baya da matasa masu kishin cigaban jam’iyyar mu ta ADC, muna mika godiya ta musamman ga Allah SWT sannan muna nuna cikakken biyayya da ladabi ga jagororinmu da shugabannin jam’iyya bisa irin kokarin da suke yi domin tabbatar da hadin kai, maslaha da cigaban jam’iyyar mu.
Bisa ga neman al’farmar jagoranmu, tsohon Minista Abubakar Malami, SAN, tare da kokarin kwamitin sulhu (Reconciliation Committee) na jam’iyya, mun amince da janyewa daga takarar neman kujerar Dan Majalisar Birnin Kebbi North domin tabbatar da hadin kai, zaman lafiya da kuma domin kara karfin jam’iyyar ADC gaba daya.
Wannan mataki ya samo asali ne saboda bukatar samar da fahimtar juna, maslaha da hadin kai tsakanin ‘yan takara da shugabannin jam’iyya domin kara karfin jam’iyyar ADC zuwa babban zaben shekarar 2027.
Muna amfani da wannan dama wajen mika godiya ta musamman ga dukkan shugabanni, magoya baya, matasa, abokai da al’ummar da s**a tsaya tare da mu tun daga farkon wannan tafiya. Goyon bayan ku, addu’o’in ku da kaunar da kuka nuna sun kasance babban abin alfahari da karfafa gwiwa a gare mu.
Haka kuma, muna kira ga daukacin matasa da magoya bayanmu da su kasance masu biyayya, hakuri da ladabi ga shugabanni, sannan mu ci gaba da hada kai da jajircewa wajen neman jama’a domin tabbatar da nasarar jam’iyyar mu ta ADC a shekarar 2027, Insha Allah.
Muna addu’ar Allah SWT Ya kara hada kanmu, Ya bawa jam’iyyar mu nasara, Ya kuma zabi mafi alkhairi ga al’ummar Birnin Kebbi North da Najeriya baki daya.
Nagode sosai.
Cmrd. Nasir Abdullahi Mai Gwandu
Aspirant, Birnin Kebbi North