20/09/2025
JAM’IYYAR ADC TA JIHAR KEBBI
SANARWA GA MANEMA LABARAI
20 Ga Satumba, 2025
SANARWA DAGA SASHE NA JIHAR KEBBI NA JAM’IYYAR AFRICAN DEMOCRATIC CONGRESS (ADC)
Mu a jam’iyyar ADC reshen Jihar Kebbi muna bayyana matuƙar ɓacin rai da damuwa bisa yadda Gwamnatin Jihar Kebbi ke nuna halin ko-in-kula da sakaci, musamman a fannin tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma!
A matsayinmu na jam’iyya da ke kishin walwalar 'yan ƙasa da kare mutuncinsu, reshen ADC na Jihar Kebbi na nuna matuƙar takaici da damuwa kan yadda gwamnati da wakilan da aka zaɓa s**a kasa nuna damuwa da halin ƙuncin da jama’a ke ciki musamman game da halin tsaro da ya taɓarɓare, da harin da aka kai kwanan nan a garin Bunza.
Wannan mummunan hari ya sake tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Kebbi da masu ruwa da tsaki a cikinta ba sa nuna wata damuwa game da tsaron lafiyar jama’ar da s**a ce suna mulka.
Zarge-zargen da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ya yi a baya suna kara samun karɓuwa a zukatan mutane. Abin da ke faruwa a yanzu na nuna cewa watakila akwai gaskiya a cikin korafinsa. Yaushe gwamnati za ta farka daga wannan sakaci? Har yaushe rayukan bayin Allah za su ci gaba da fuskantar haɗari, alhali gwamnati na da iko da albarkatun da za ta magance matsalar?
Muna kuma ƙara bayyana ɓacin rai kan shiru da rashin aikin da wakilanmu a matakin jiha da tarayya ke nunawa. Wannan ne lokacin da ya kamata su tashi tsaye, su ji tsoron Allah, su tsaya tsayin daka wajen kare mutanen da s**a zaɓe su. Amma saboda yawancinsu ba su samu kujerunsu da sahalewar jama’a ba, sun zaɓi yin shiru, su jingina a gefe.
Sau da dama idan aka s**ar gwamnati, sai a ga sun fito da gaggawa suna kare kansu a kafafen yada labarai. Amma yanzu da aka rasa rayuka a Bunza, ba ma guda ɗaya daga cikin shugabanni ya fito ya yi magana. Wani irin shugabanci ne wannan? Sai mutum ya zama mai iko ko sananne kafin a ba da muhimmanci ga rayuwarsa?
Muna tunatar da Gwamnatin Jihar Kebbi cewa rayukan jama’a amana ne daga Allah da aka ɗora musu. Babu