20/12/2025
A yau, jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) reshen Yobe State ta gudanar da taron tuntuba na kowane makonni biyu kamar yadda tsarin jam’iyyar ya tanada. An gudanar da taron a sakatariyar jam’iyyar ta jiha da ke Damaturu, Jihar Yobe.
Taron ya haɗa manyan jami’an jam’iyyar a matakin jiha da ƙananan hukumomi, wakilan abokan haɗin gwiwa (coalition partners), da sauran mambobin jam’iyyar daga sassa daban-daban na jihar. Manufar taron ita ce tattaunawa, daidaita tsare-tsare, da ƙarfafa haɗin kai tsakanin shugabanni da mambobin jam’iyyar.
A jawabin buɗe taro, Shugaban Jam’iyyar ADC na Jihar Yobe ya yi maraba da mahalarta tare da gode musu bisa jajircewa da sadaukarwar da suke nunawa wajen bunƙasa jam’iyyar. Ya jaddada muhimmancin haɗin kai, bin doka da oda, da ci gaba da tuntuba domin ƙarfafa tsarin jam’iyyar da faɗaɗa tushenta a matakin ƙasa.
Muhimman batutuwan da aka tattauna sun haɗa da
Nazari kan halin siyasa na baya bayan nan a matakin jiha da ƙasa baki ɗaya.
Bita kan ayyukan jam’iyyar tun bayan taron da ya gabata.
Ƙarfafa haɗin gwiwa da abokan haɗin jam’iyya domin cimma muradun bai ɗaya.
Tsare tsaren ƙara yawan mambobi, wayar da kan jama’a, da ƙarfafa ayyukan jam’iyya a matakin mazabu da ƙananan hukumomi.
Shirye shirye da tanade tanade kan shirye shiryen jam’iyyar na gaba.
Wakilan abokan haɗin gwiwa sun tabbatar da aniyarsu ta ci gaba da aiki kafada da kafada da ADC domin samar da dimokiraɗiyya ta gaskiya, adalci, da shugabanci nagari. Haka kuma, mambobin jam’iyyar sun gabatar da shawarwari masu amfani da nufin inganta tsarin jam’iyya, sadarwa, da kusanci da al’umma.
Sign:
Yobe ADC media Team.