20/09/2025
Adam Ashaka inason kasani-
Sheikh Muhammadu Sani Yahaya Jingir ya shahara a Najeriya da wajen ta a matsayin babban jagoran Izalah (JIBWIS), kuma ɗaya daga cikin fitattun Malaman Musulunci da s**a tsayu wajen yada tauhidi da da’awa cikin gaskiya da jajircewa.
Tun daga ƙuruciya, ya sadaukar da rayuwarsa wajen neman ilimin addini da koyar da shi ga jama’a. Da zarar ya shiga harkar tafsiri da wa’azi, ya zama haske ga al’umma, inda jama’a ke komawa gare shi don samun shiriya da ilim
Gudummawa da Ayyukan Da Ya Assasa.
Sheikh Jingir ya zama ginshiƙi wajen samar da ilimi, lafiya, da cibiyoyin addini a Najeriya da wajen ta.
Makarantu: ya assasa makarantu sama da 1000 – daga matakin firamare, sakandire, Malja’ussunnah Colleges, har zuwa manyan cibiyoyi na gaba da sakandire.
Jami’a: ya kafa Fortune University, wadda ta zama ginshiƙi wajen bai wa Musulmi damar samun ingantaccen ilimi mai hade addini da zamani.
Lafiya: ya bude cibiyoyin lafiya da dama, ciki har da Teaching Hospital, domin tallafa wa al’umma wajen kiwon lafiya.
Izalah: ya yada cibiyoyin Izalah a dukkan jihohin Najeriya da yawancin ƙananan hukumomi, lamarin da ya sa ƙungiyar ta zama mafi girma a nahiyar Afrika.
Musabaqar Al-Qur’ani: ya assasa cibiyoyin musabaqar Qur’ani a dukkan sassan Najeriya da ma kasashen Afrika, domin inganta karatun Qur’ani da fassara.
Da’awa ta Matasa: ya jagoranci cibiyoyin da’awar matasa, yana ba su jagora da shiriya wajen tunkarar ƙalubale na zamani.
Masallatai da Majalisai: ya kafa dubban masallatan Juma’a, masallatan kamsu salawatu, da darussa na ilimi a fannoni daban-daban.
Juriyar Gwaji da Wahalhalu
Sheikh Jingir ya sha gwagwarmaya a lokacin rikicin Jos da wasu rikice-rikice na ƙasa:
An jefa masa bama-bamai a gidansa da cibiyoyin da’awarsa.
Ya fuskanci barazana daga abokan gaba na cikin gida da na wajen ƙasa.
Duk da haka, ya ci gaba da tsayawa yana jagorantar jama’a, ba tare da tsoro ko kasawa ba.
Tasirin Da’awa da Jagoranci
A yau, ana kiyasta cewa mabiya Sheikh Jingir sun kai fiye da miliyan 40 a Najeriya, tare da fiye da miliyan 12 a ƙasashen waje.
Wannan yawan mabiya ya nuna irin amincewa da karɓuwa da yake da shi, da yadda muryarsa take da tasiri a kan al’umma.
Maganarsa tana da nauyi har ta kai ga cewa duk wani makiyi na Musulunci ko kuma mai adawa da gaskiya yana jin tsoron furucinsa, musamman idan ya yi magana a kan wani muhimmin lamari da ya shafi kasa baki É—aya.
Yana daga cikin fitattun Malamai masu ƙarfi wajen yin magana kan siyasa, zamantakewa, da addini cikin gaskiya da amana.
Da’ar Mabiya
Ɗaya daga cikin abubuwan da s**a fi fito da Sheikh Jingir a matsayin jagora shi ne tsarin da mabiya s**a kafa bisa Qur’ani da Sunnah:
Da’a ɗaya: duk inda ka sami mabiya Sheikh Jingir a Najeriya ko a Afrika, zaka tarar da akida iri ɗaya – akidar tauhidi bisa fassarar magabata na kwarai (salaf).
Biyayya: mabiya ba sa bijirewa umarninsa, domin sun san cewa dukkan umarnin nasa yana da hujja daga Qur’ani da Hadisi.
Tsari na gama-gari: wannan ya sanya ƙungiyar Izalah ta zama ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da s**a fi samun nasarar haɗa Musulmi a tsari ɗaya, ba tare da rikice-rikicen akida ba.
Tasirin shugabanci: da’arsa ta wuce Najeriya ta shiga kasashen Afrika daban-daban, inda mabiya ke gudanar da ayyuka bisa tsarin da ya shimfiɗa.
Jagoranci na Gaskiya
Sheikh Jingir ya kasance:
1. Mai tsayin-daka a kan tauhidi da Ahlus-Sunnah wal-Jama’a.
2. Mai gina cibiyoyi da s**a inganta rayuwar Musulmi ta fannoni da dama (ilimi, lafiya, ibada).
3. Mai tasiri a duniya – inda maganarsa ke shiga kunne har zuwa kasashen waje.
4. Mai É—aukaka martabar Musulunci a idon duniya ta hanyar jagoranci mai gaskiya.
✍🏽 Suleiman Abubakar Yuguda