13/04/2026
Assaalamu Alaikum...
Al'ummar faskari baki daya da jama'a na karamar hukumar faskari dukkan su mutanena ne kuma yan uwana ne.
Dukkan wards din faskari guda goma Ina daukar su matsayin yan uwa na jini, ko a nan gida ko a waje duk Wanda ya fito daga karamar hukumar faskari to dan uwan Samaila Muazu ne.
Munyi mu'amular azuki da mutanen faskari tun daga matakin yarinta, zuwa karatun primary har zuwa inda muke yanzu, bamu taba nuna rashin jindadi ga kowa ba, har zuwa shigar mu takara mun tsaya mun zauna lafiya da kowa, bamu Sanya kowa yaci mutumcin wani ko wasu ba, idan ma wani yayi aka sanar damu nan take zamu kira shi mu tsawatar masa, duk yaran mu sun San wannan.
Dangane da maganar da aka shirya aka ce daga bakin Samaila Muazu ta fito akan al'ummar mu na garin mairuwa, ni Engr SMB Ina mai nesanta kaina daga wannan zance ban san inda aka samo shi ba, sai dai naji kuma na gani a media, bayan nan Ina Kara tabbatar ma kowa cewa ba faskari ba, ko kasar wajene indai akwai yan uwa musulmai ba zan taba iya yi masu kudin goro na zage su ba, ba hali na bane ba dabi'a ta bace, b***e kuma garin mairuwa wurin da nake da abokan karatu, yan uwa na jini, yarana, iyaye na, malamai na, da sauran masoya.
Wannan magana an tsire ta ne domin a bata Mani suna a mairuwa, amma wallahi bani da masaniyya akan duk abunda aka fadi.
Allah SWT ya Kara tsare mu ya tsare mana imanin mu ya karo mana zaman lafiya da hadin kai baki daya nagode.
Hon SMB....