Youths For RADDA Vision

Youths For RADDA Vision This is an official page of the youths For RADDA Vision.

Kungiyar Youth for Raɗɗa Vision ta Ƙaramar Hukumar Bakori ta halarci bikin ƙaddamar da aikin gina hanyoyin cikin gari gu...
22/07/2026

Kungiyar Youth for Raɗɗa Vision ta Ƙaramar Hukumar Bakori ta halarci bikin ƙaddamar da aikin gina hanyoyin cikin gari guda tara (9) masu tsawon kilomita 6.6km, wanda Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, PhD, CON, ya ƙaddamar.

A yayin wannan gagarumin biki, shuwagabannin kungiyar na Ƙaramar Hukumar Bakori sun samu ganawa da jigo kuma jagoran kungiyar baki ɗaya, Hon. Abdulkadir Mamman Nasir, Chief of Staff na Jihar Katsina, inda s**a sake jaddada cikakken goyon bayansu ga manufofin gwamnatin APC da kuma tabbatar da aniyarsu ta mara wa duk wani ɗan takarar Jam'iyyar APC baya a dukkan zaɓuɓɓukan da ke tafe.

Kungiyar ta bayyana cewa za ta ci gaba da wayar da kan matasa, haɗa kan al'umma, da kuma aiki tukuru domin tabbatar da nasarar Jam'iyyar APC tare da ci gaban Jihar Katsina da Ƙaramar Hukumar Bakori baki ɗaya.

Kimanin Hanyoyi guda 20 Gwamna Radda Ya Kaddamar da Fara Aikin su a Cikin Garin Malumfashi wanda zasu laƙume fiye da Nai...
22/07/2026

Kimanin Hanyoyi guda 20 Gwamna Radda Ya Kaddamar da Fara Aikin su a Cikin Garin Malumfashi wanda zasu laƙume fiye da Naira Biliyan 10.

A ranar Talata 21/7/2026, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya za'a harsashen fara aikin gina hanyoyin guda (20) masu tsawan kilo mita 10.7 a cikin garin Malumfashi,a wani bangare na gwamnatinsa na inganta garuruwa a fadin jihar Katsina.

Kamfanin Mothercat Limited ne zai gudanar da aikin, yayin da Ma’aikatar Ayyuka, Gidaje da Sufuri ta Jihar Katsina za ta sa ido domin tabbatar da inganci da bin ƙa’idojin aikin.

Da yake gabatar da jawabin shi Gwamna Radda ya bayyana cewa aikin ya kasance amsa ga wata muhimmiyar buƙata da al’ummar Malumfashi s**a daɗe suna nema ta inganta hanyoyin sufuri a yankin.

Gwamnan yaci gaba da cewa" Samar da ingantattun hanyoyi zai taimaka wajen sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a da jigilar kayayyaki, bunƙasa harkokin noma da kasuwanci, inganta tsaro, tare da ƙara haɓaka ayyukan tattalin arziki a cikin garin Bakori da kewaye.

Gwamnan ya bayyana cewa aikin wani ɓangare ne na babban shirin gwamnatinsa na sauya fasalin al’umma ta hanyar zuba jari mai ma’ana a fannonin samar da hanyoyi, ilimi, kiwon lafiya, noma, samar da ruwa, tsaro da bunƙasa tattalin arziki.

Ya jaddada cewa ci gaba dole ne ya shafi dukkan sassan Jihar Katsina, yana mai bayyana cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da ayyukan da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar al’umma a dukkan ƙananan hukumomi 34 na jihar.

Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri na Jihar Katsina, Injiniya Dakta Sani Magaji Ingawa, ya bayyana cewa aikin na nuna ƙudirin Gwamna Radda na samar da abubuwan more rayuwa da suke amfanar jama’a.

Kwamishina yace" an zaɓi hanyoyin ne domin magance matsalolin zirga-zirga da al’ummar Bakori ke fuskanta, inda ya tabbatar da cewa ma’aikatar za ta tabbatar da cikakken sa ido domin ganin an gudanar da aikin yadda ya kamata, bisa ƙa’idojin da aka tsara da kuma kammala shi cikin lokaci.

Engr Sani Magaji ya ƙara da cewa haɗa fitilun hasken rana a cikin aikin na nuna yadda gwamnatin jihar ke mayar da hankali wajen samar da ababen more rayuwa masu ɗorewa, waɗanda za su ƙara tsaro tare da tallafa wa harkokin kasuwanci da sauran ayyukan tattalin arziki musamman da dare.

A nashi jawabin, wakilin kamfanin Mothercat Limited, kamfanin da ke gudanar da aikin, ya nuna godiyarsa ga gwamnatin Jihar Katsina bisa wannan dama, tare da yin alƙawarin kammala aikin cikin inganci da bin ƙa’idojin da aka amince da su a cikin lokacin da aka tsara.

Ya tabbatar da cewa kamfanin zai samar da ƙwararrun ma’aikata, kayan aiki da dukkan abubuwan da ake buƙata domin ganin aikin ya yi nasara, tare da yin aiki kafada da kafada da ma’aikatar da kuma al’ummar yankin.

Da yake magana a madadin al’ummar Malumfashi, Shugaban Karamar Hukumar Malumfashi Hon Muntari City, ya yaba wa Gwamna Radda bisa amincewa da wannan aiki, yana mai bayyana shi a matsayin gagarumar gudummawa da za ta inganta harkokin sufuri, kasuwanci da walwalar jama’ar yankin.

Ya kuma tabbatar da haɗin kan al’umma wajen ba da goyon baya ga kamfanin da kuma kare wannan muhimmin aikin bayan kammalawa.

Shima Sanatan Katsina ta Kudu, Sanata Muntari Dandutse, ya yabawa gwamnan bisa wannan gagarumin aiki tare da tabbatar da goyon bayan al’ummar yankin don samun nasarar aikin.

Mutane da dama s**a tofa albarkacin bakinsu daga ciki akwai Galadiman Katsina Hakimin Malumfashi Mai Shari'a Sadiq Abdullahi Majiya, shugaban ƙaramar hukumar Malumfashi Hon. Muntari City.

Taran ya samu halartar Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Rt. Hon. Nasir Yahya Daura, Sanatan da ke wakiltar Katsina ta Kudu (Funtua), Sanata Muntari Dandutse, Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Katsina, Dakta Bishir Gambo Saulawa,

Sauran sun haɗa da tsohon sanatan shiyyar Funtua Sanata Bello Mandiya, Kwamishina ta harkokin mata Hon. A'isha Aminu Malumfashi, shugabannin ƙananan hukumomi, ‘yan majalisu, sarakunan gargajiya, mambobin Majalisar Zartarwa ta jihar, manyan jami’an gwamnati, shugabannin siyasa, wakilan al’umma; da shugabanni da ma’aikatan kamfanin Mothercat Limited.

20/07/2026

Masha Allah

Alhamdullillah Masha Duk Acikin Shirin Tarbar Mai Girma Gwamnan JAHAR Katsina Zuwa MALUMFASHI,Bakori, Funtua Insha Allah
20/07/2026

Alhamdullillah Masha

Duk Acikin Shirin Tarbar Mai Girma Gwamnan JAHAR Katsina Zuwa MALUMFASHI,Bakori, Funtua Insha Allah

ASSALAMU ALAIKUM WA RAHMATULLAHI WA BARAKATUHSanarwa ga Dukkan Mambobin YOUTHS FOR RADDA VISSIONAna sanar da dukkan mamb...
20/07/2026

ASSALAMU ALAIKUM WA RAHMATULLAHI WA BARAKATUH

Sanarwa ga Dukkan Mambobin YOUTHS FOR RADDA VISSION

Ana sanar da dukkan mambobin ƙungiyarmu cewa gobe Talata, 21 ga Yuli, 2026, Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, zai jagoranci ƙaddamarwa da fara ayyukan manyan tituna a Funtua, Bakori da Malumfashi kamar yadda Ma'aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jihar Katsina ta sanar.

Saboda haka, ana gayyatar dukkan mambobin YOUTHS FOR RADDA VISSION da su fito cikin taro domin nuna goyon baya ga wannan gagarumin ci gaba da gwamnatin Malam Dikko Umaru Radda ke kawo wa al'ummar Jihar Katsina.

🗓 Rana: Talata, 21 ga Yuli, 2026
🕙 Lokaci: Daidai da lokacin da ya shafi yankinku (10:00 na safe, 1:00 na rana ko 4:00 na yamma).

Mu fito cikin tsari, da ladabi, tare da nuna haɗin kai da goyon bayan cigaban Jihar Katsina.

Nagode.
YOUTHS FOR RADDA VISSION
Leadership

17/07/2026

Gwamna Radda Ya Kai Ziyarar Ta'aziyya ga Shugaban Karamar Hukumar Ingawa Bisa Rasuwar Mahaifiyarsa

Bayan kammala Sallar Juma'a a garin Ingawa, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya kai ziyarar ta'aziyya ga Shugaban Karamar Hukumar Ingawa, Hon. Abubakar Idris (02), bisa rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Maryama Idris Sanda.

A yayin ziyarar, an gudanar da addu'o'in neman gafara da rahama ga marigayiyar, tare da roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta mata kurakuranta, Ya karɓi bakuncinta, Ya sanya ta cikin Aljannatul Firdausi. Haka kuma, Gwamnan ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga iyalan mamaciyar, musamman ga Shugaban Karamar Hukumar Ingawa da mahaifinsa, Alhaji Idris Sanda, tare da addu'ar Allah Ya ba su juriyar jure wannan babban rashi.

A wannan ziyara, Gwamnan ya samu rakiyar Shugaban Ma'aikatan Gidan Gwamnatin Jihar Katsina, Alhaji Abdulkadir Mamman Nasir; PPS, Hon. Abdullahi Aliyu Turaji; ɗan takarar kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Kankia/Ingawa/Kusada a Jam'iyyar APC, Hon. Mustapha Kanti; ɗan takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Katsina mai wakiltar Ingawa a APC, Hon. Akilu Mamman Yandoma; jigo a Jam'iyyar APC a Karamar Hukumar Ingawa, Alhaji Sule Aruwa; Dr. Bilyaminu Sulaiman, Shugaban Kamfanin ABILS; da sauran masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar APC a karamar hukumar.

Allah Ya jikanki Hajiya Maryama Idris Sanda, Ya gafarta mata, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarta. Amin.

17 ga Yuli, 2026.

Dr. Dikko Umaru Radda administration has been actively involved in empowering youths through various initiatives under t...
16/07/2026

Dr. Dikko Umaru Radda administration has been actively involved in empowering youths through various initiatives under the "Youths For RADDA Vision" umbrella, focusing on skills acquisition, entrepreneurship, and self-reliance.

As of December 2024, The Katsina Youth Craft Village. (K.Y.C.V) has been positioned as a leading institution for vocational training, with 634 young men and women graduating with practical skills and starter packs in trades like tailoring, carpentry, and ICT.

The governor has emphasized the importance of equipping youths with relevant skills to drive economic growth and job creation. In line with this vision, the state government has partnered with organizations like the Family Homes Fund to train youths in masonry, electrical wiring and other skills, providing them with starter packs and database registration for future engagement.

Additionally, Governor Radda's administratior has implemented programs like the Katsina State Enterprise Development Agency (KASEDA) in partnership with the National Automobile Technicians Association (NATA Mechatronics Apprenticeship Programme empowering 1,169 youths with practical skills and starter packs as of April 2026.

To further support youth development, the state government has also launched Initiatives like the "Building Your Future" youth development and empowerment program, which disbursed N252 million to over 1,000 young entrepreneurs in February, 2025.

With these efforts, Governor Radda's administration aims to create a skilled and empowered population that can drive economic growth and development in Katsina State.

16/07/2026

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya miƙa kyautar motoci ƙirar Peugeot 206 ga Mafi Hazakar Ɗalibi (Best Graduating Student) a lokacin bikin yaye ɗaliban Jami'ar Al-Qalam.

Haka kuma, Mai Girma Gwamnan ya karrama Gwani da Gwana da s**a yi zarra a Musabaƙar Al-Qur'ani ta makarantar, a matsayin ƙarfafa gwiwa ga neman ilimi da kuma hidimtawa Al-Qur'ani Mai Girma.

Wannan wani abin a yaba ne da ke nuna yadda gwamnatin Malam Dikko Umaru Radda ke ba ilimi da kyautata ɗabi'a muhimmanci, tare da ƙarfafa matasa su ƙara himma wajen neman ilimi da samun nasara.

Kungiyar da rajin tabbatar da nasarar gwamnatin APC a jihar Katsina a zaben 2027, YFRV Ta Yi Taron Dabarun Wayar da Kai ...
16/07/2026

Kungiyar da rajin tabbatar da nasarar gwamnatin APC a jihar Katsina a zaben 2027, YFRV Ta Yi Taron Dabarun Wayar da Kai domin samar da hanyoyin tallata Ayyukan Gwamna Raɗɗa da kuma kokarin da take yi wajen magance Matsalolin Tsaro

Ƙungiyar Youth for Radda Vision (YFRV), ƙarƙashin jagorancin Hon. Abdulkadir Mamman Nasir, shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin Jihar Katsina (Chief of Staff), ta gudanar da taron ta da nufin ƙara azamar mambobinta domin ci gaba da wayar da kan al'umma kan ayyukan ci gaba da gwamnatin Malam Dikko Umaru Raɗɗa ke aiwatarwa.

A yayin taron, mahalarta sun jaddada muhimmancin ci gaba da bayyana wa jama'a irin nasarorin da gwamnatin jihar ke samu a fannoni daban-daban, tare da kira ga al'umma da su guji yadda wasu na amfani da batun tsaro wajen siyasa domin cimma muradunsu.

Ƙungiyar ta kuma buƙaci al'umma da su ci gaba da yin addu'o'i domin Allah Ya kawo ƙarshen matsalolin tsaro da kuma sauƙaƙa wa jama'a matsin rayuwa da ake fuskanta.

Haka kuma, an ƙara ma matasan jihar azama da su cigaba da mayar da hankali wajen neman halal da dogaro da kai, su guji aikata duk wani abu da zai jawo musu nadama a nan gaba, tare da kasancewa masu bayar da gudunmawa wajen gina makomar Jihar Katsina.

Ƙungiyar ta bayyana cewa ci gaban Jihar Katsina alhakin kowa ne, don haka ya zama wajibi gwamnati da al'umma su haɗa kai domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa.

Mukhtar Umar Dandume
Zonal Public Relations Officer
Youths For Radda Vission 2027

16/07/2026

Youths For Radda Vission

Address

Funtua LGA
Funtua

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Youths For RADDA Vision posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share