02/12/2025
🎙️ MEKESAWA TV – LABARI NA MUSAMMAN
Babu Sabon Umurnin INEC Kan Ajiyar Mukami Kafin 2026 Primaries — Binciken Mu Ya Gano
A kwanakin nan an ta yada labarin cewa Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) ta umarci duk masu rike da mukaman gwamnati da ke shirye-shiryen tsayawa takara a shekarar 2026 da su ajiye kujerunsu tun daga watan Fabrairu 2026.
Amma binciken da Mekesawa TV ta gudanar ya tabbatar da cewa:
📌 Babu wata sanarwa daga INEC da ta ayyana irin wannan sabuwar doka.
📌 Sanarwar da ake jingina wa hukumar ba ta bayyana a kowane dandamali na INEC ba — ko shafin intanet, ko takardun watsa labarai, ko kafofin sada zumunta.
A bangaren doka, sashi 84(12) na Electoral Act 2022 shi ne ya tanadi cewa masu rike da mukaman siyasa ba za su shiga fidda gwani ba sai sun sauka daga mukamansu. Sai dai tun a 2022, Kotun Daukaka Kara ta dakatar da aiwatar da wannan tanadi, tana mai cewa ya saba wa kundin tsarin mulki.
Tun daga wannan hukunci zuwa yau, ba a sake tabbatar da wannan tanadi ba, kuma INEC ba ta sake fitar da wata sabuwar doka da ta sabunta shi ba.
Masu nazarin siyasa sun shaida cewa ko da ba tilas bane daga INEC, jam’iyyu na iya zabar saka irin wannan sharadi a cikin tsarin cikinsu domin tabbatar da adalci ko kuma tsare-tsaren cikin gida.
Yayin da ake matsowa ga shekarar zabe ta 2026, wannan batu ya fara daukar hankali, kuma zai ci gaba da tayar da muhawara tsakanin masu neman tikitin takara da magoya bayan su.
📺 Ku cigaba da bin MEKESAWA TV — mu na kawo muku gaskiyar labarai ba tare da hayaniya ba.