Ministry For Religious Affairs Zamfara State

Ministry For Religious Affairs Zamfara State for God and Humanity

FASARAR HUDUBAR MASSALACIN JUMUAH NA UMAR IBN ABDILAZIZ ALBARKAWA GUSAU, TA RANAR JUMUAH 5/12/1447.22/5/2026.TAKENTA SHI...
22/05/2026

FASARAR HUDUBAR MASSALACIN JUMUAH NA UMAR IBN ABDILAZIZ ALBARKAWA GUSAU, TA RANAR JUMUAH 5/12/1447.22/5/2026.

TAKENTA SHI: Layya da Abinda ta kunsa.

Godiya ta tabbata ga Allah Wanda yake cewa Kuma maganarsa gaskiya ce "Jininda kuke yankawa ko Naman bashi ne yake kaiwa ga Allah ba, saidai Jin tsoron Allah dinku shi yake samunsa".
Kuma Ina shaida Babu abin bauta bisa can canta sai Allah shikadai yake ba yada abokin tarayya Wanda yake shikadai abin nuhi da bukatu, Kuma Ina shaida lallai Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi wasallam bawansa ne Kuma manzonsa ne Wanda aka Aiko da shiriya da Rahma da Bushara, Allah kayi salati da Albarka garesa da iyalansa da sahabbansa da matayensa da zuriyarsa kamar yadda kayi salati da Albarka ga Ibrahim Kai abin yabo ne Mai Girma.

Bayan haka "Hakika Allah ya bada labari Kuma Bai gusheba yana Mai Girma cewa yanka na ibada da zubarda jini da sunan Allah Bai gusheba yana abin sharantawa cikin sharioinda s**a gabata "Kowace Alumma mun Sanya mata ibadar yanka domin su ambaci sunan Allah bisa abinda ya arzurta su dashi daga Dabbobin nima abin bautarku abin bauta guda ne ku Mika wuya garesa".

Abin nuhi mun sharanta ga alummomin da s**a gabata tun zamanin Ibrahim Aminci ya tabbata garesa zuwa wadanda s**azo bayansa wasu nauo'in ibadu Kuma ya Sanya dalilin yin haka su ambaci sunan Allah Wanda dunayensa sun tsarkaka ga ibadodi abin bauta guda ne Koda abinda aka dorawa halittu ya ban banta saboda ban bantuwar zamani da mutane da wuri saboda banbantuwar maslaha, kada ku ambaci sunan Wanin Allah ga yankan ku ku tsarkake ibada garesa shikadai ta yadda Babu wata shirka da zata shigesa gaba daya.

Ibn Abi Hatim ya ruwaito cewa "Mutanen jajhiliyya suna kawo nama a daki Mai tsarki sai sahabbai s**ace mu mukahi can canta da wannan sai Allah ya saukarda "Amanda kuke yankawa ko jinin bashi ne yake zuwa ga Allah ba,saidai Jin tsoron Allah dinku shi yake kaiwa garesa".

Ita layya an sharanta muku ita domin ku ambaci Allah sadda zaku yankata domin shine Mai arzurtawa mahalicci ba abinda yake zuwa wajensa na nama ko jini, shi Allah madaukakin mawadaci ne daga duk Wanda bashi ba.
Layya ta tabbata ta Hanyoyi ukku wato maganar Annabi aikinsa da Kuma tabbatarwarsa.
Domin ya kwadaitar da yin layya Kuma yayi umurni da ita.

Ibn Maja ya ruwaito daga zaid ibn Arkam yace, nicce ya manzon Allah wagga layyar da mukeyi minene matsayinta? Sai yace sunnar babanku Ibrahim ce, sai s**ace inmunyita mi zamu samu? Sai yace Kowane gashi Allah zai Baku Lada,sai s**ace Sufi hwa? Sai yace Kowane Sufi Lada ne".

Kamar yadda Tirmizi ya ruwaito cewa "Ba Wani aiki da mutum zaiyi ranar s**a Wanda Allah yake so kamar zubarda jini,zaizo ranar Alkiyama da kahoninsa da kohwatonsa da gashinsa, Kuma jini yana zuwa wajen Allah kahin ya zuba kasa ku yita domin Allah ".

Amma aikinsa, Muslim ya ruwaito daga Aisha Allah ya yarda da ita cewa Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yace a kawo masa rago Mai kahoni Mai takawa cikin Baki Mai kallo cikin Baki sai akazo masa dashi domin yayi layya dashi, sai yace mata kawomin Yuka sannan yace kodamin ita saita Koda ta ga dutsi sai ya karba ya kwantarda ragon sannan ya yanka yace da sunan Allah Allah ka karbama Muhammad da alummar Muhammad sannan yayi layya dashi.
Amma tabbatarwarsa ya kasance sahabbansa suna yin layya yana gani Kuma ya tabbatarda su akan haka".

Jundub ibn Sufyan yace "Na halarci sallar layya tareda manzon Allah Sallallahu Alaihi wasallam lokacinda ya kare sallah da mutane sai ya Kalli ragunan duk an yanke sai yace Duk Wanda ya yanke kahin sallah to ya sake Wanda Kuma Bai yanka ba to ya yanka da sunan Allah ".
Cewa layya wajibi ce ga Wanda ya Sami iko yahi karhi domin tana cikin Alamomin Addini, Kuma domin Allah ya sharanta ta ga Wanda ba makka yake ba domin samun dai daito ga bayi cikin samun kusanci zuwa ga Allah ta hanyar sokewa cikin kowane gari, wannan yana cikin nimar Allah da rahmarsa, kamar yadda Wani Bai iya zuwa Makkah domin yanka hadaya sai aka Sanya layya duk inda mutum yake a duniya, ita tana cikin Alamomin Addinin Allah.

Wassalamu Alaikum warahmatullahi

Imamu Bashir Siraj Gusau.

22/05/2026
22/05/2026

Wa'azin Mako Mako a Mako na (1,313)
Tare da Dr. Aminu Umar Gummi

Mai Taken : FALALAR KWANAKKI GOMA NA FARKON WATAN ZULHIJJAH

Assalamu Alaikum warahmatullahJadawalin watan Musulunci na ZULL HAJJ na Shekarar Musulunci ta 1447AH.Muna Roqon Allah ya...
19/05/2026

Assalamu Alaikum warahmatullah

Jadawalin watan Musulunci na ZULL HAJJ na Shekarar Musulunci ta 1447AH.

Muna Roqon Allah ya kawo mana Zaman lafiya da aminci a Jahar mu ta zamfara dama kasarmu Baki dayah.

Daga Dan uwanku: Zaharaddeen Zarumee Gusau.

FASARAR HUDUBAR MASSALACIN JUMUAH NA UMAR IBN ABDILAZIZ ALBARKAWA GUSAU, TA RANAR JUMUAH 28/11/1447H.15/5/2026D.TAKENTA ...
15/05/2026

FASARAR HUDUBAR MASSALACIN JUMUAH NA UMAR IBN ABDILAZIZ ALBARKAWA GUSAU, TA RANAR JUMUAH 28/11/1447H.15/5/2026D.

TAKENTA SHI NE: FALALAR KWANAKKI GOMA NA HWARKON WATAN ZULHIJJAH.

Godiya ta tabbata ga Allah abun yabo Mai Girma mabucin falala da kyautatawa Wanda ya daga lokuttan biyayya ga Allah yake lunka Lada cikin su,Ina gode maSa Ina yabonSa Kuma Ina shaida Babu abin bauta bisa can canta sai Allah shikadai yake ba yada abokin tarayya Kuma Ina shaida lallai Annabi Sallallahu Alaihi wasallam bawansa ne Kuma manzonsa ne, mahihicin Wanda yayi sallah yayi azumi ya ambaci Allah yayi tsayuwar dare, Allah kayi salati garesa da iyalansa da sahabbansa da wadanda s**abi hanyarsa har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka:- Kuji tsoron Allah yaku bayin Allah domin Jin tsoron Allah shine mahi girman Guzuri domin ranar sakamako, madaukakin sarki yana cewa "Kuma kuyi Guzuri lallai mahi girman Guzuri shine Jin tsoron Allah".

Yaku musulmi Hakika Allah ya sanyawa bayinsa lokutta masu Girma wadda zasuyi guzurin biyayya ga Allah cikin su, suyi ridge rige cikin yima Allah biyayya yana cikin wadannan kwanakki da Ake rige rige cikin su wajen samun yardar Allah kwanakki goma na hwarkon Watan zulhijjah kwanakki da Allah yayi rantsuwa dasu cikin littahinsa yana cewa "Ina Rantsuwa da alfijiri da darare goma".

Haduwar masu tafsirin sun tahi cewa sune kwanakki goma na hwarkon Watan zulhijjah.
Annabi Sallallahu Alaihi wasallam ya bayyana falalar wadannan kwanakki yana cewa" Babu wasu kwanakki wadanda s**ahi soyuwa wajen Allah sama da wadanga kwanakki goma s**ace Koda jihadi ya manzon Allah? Sai yace Koda jihadi saboda Allah sai mutumenda ya hita da ransa da dukiyarsa Bai dawo da komi ba".

Yaku bayin Allah kwanakki ne Yan kadan Amma Allah ya girmama Lada cikin su sama da wasu kwanakki wadanda ba su ba, Kuma Allah cikin hikimarsa ya Tara ibadodi masu yawa cikin wadannan kwanakki sallah da azumi sadaka Hajji zikiri karatun Alkura'ni Da'a ga Allah da kyautatawa bayin Allah.

Cikin ayukka masu darajja cikin wadannan kwanakki:

1.Yawaita ambaton Allah,madaukakin sarki yana cewa"Kuma su ambaci Allah cikin kwanakki sanannu".

Kuma Abdullahi Dan Umar da Abu Huraira Allah ya yarda dasu sun kasance suna hita kasuwa suna kabbarori, mutane na yin kabbarori da kabbarorin su.

Domin haka Ku raya wannan Sunna da aka kauracema ku yawaita kabbarori cikin wadannan kwanakki.

2. Azumi kebance azumin yinin Arfah ga Wanda ba Alhaji ba, Hakika Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yace"Ina tsammani ga Allah yana karkare zunubin shekararda ta gabata, da wadda zata zo".

Dubi irin wannan kasuwanci Mai Riba azumin yini guda ya karkare zunubin shekaru biyu.

3.Tuba ta Gaskiya, Mai hankali shine Wanda zai ribanci lokuttan Alkairi kahin dama ta wuce, ya koma zuwa ga ubangijinsa kahin saukar ajalinsa.

Da yawa daga cikin mutanenda bara Muna tareda su yanzu Kuma suna karkashin kasa, Mai lahiya nawa ne yau bashida lahiya, rayayye nawa ne yau yana cikin kabari? Don haka Ku tuba zuwa ga Allah Baki daya yaku masu Imani domin ku Sami babban rabo.

4. Sadaka da kyautatawa , cikin wadannan kwanakki Allah na lunka Lada ga ayukkan kwaraiŘŚmusamman ciyarwa, ku taimakawa talakawa ku ciyarda mabukata ku Sanya hwarin ciki cikin su.

5. Ibadar layya,ita layya tana cikin Alamomin Addini masu Girma Kuma sunnace Mai karhi ga Wanda Allah Yaba iKon, Allah madaukakin sarki yana cewa "Kayi sallah domin ubangijinka Kuma ka soke layyarka".

Ya kamata ga musulmi yayi kwadayin aikata wannan Sunnah in Allah ya bashi dama.
Yaku musulmi hasara ce babba ga mutum wadannan kwanakki su wuce mutum baiyi komi na Alkairi ba.

Kuma cikin abinda ya kamata musulunci su kula dasu cikin wadanga kwanakki,gyara zuciya domin Allah baya kallo zuwa ga surorin jikin mu ko dukiyoyin mu, sai dai yana kallo zuwa ga zukatan mu da ayukkan mu, don haka Ku tsarkake zukatan ku daga hassada da kiyayya da juna ku nisanci yanke zumunta ku kyara abinda ya Baci tsakanin ku ku kyautatawa makwabtaka.
Da karshe yaku bayin Allah an sunnanta ga duk Wanda zaiyi layya ya kame daga aski ko yanke akaihu da anga wata sai bayan yayi layya.

Allah kabamu iKon anhwanuwanda wadanga kwanakki masu Albarka...

Kadan Daga Cikin hotunan Mahalarta wa'azin Mako mako na wannan sati na (1,312),Wanda Dr. Rabiu Shehu  Ya gabatar....
15/05/2026

Kadan Daga Cikin hotunan Mahalarta wa'azin Mako mako na wannan sati na (1,312),

Wanda Dr. Rabiu Shehu Ya gabatar....

15/05/2026

Live streaming of Zaharaddeen Zarumee Gusau

Kadan Daga Cikin hotunan Mahalarta wa'azin Mako mako na wannan sati na (1,311),Wanda Sheikh Salihu Liman kaura. Ya gabat...
09/05/2026

Kadan Daga Cikin hotunan Mahalarta wa'azin Mako mako na wannan sati na (1,311),

Wanda Sheikh Salihu Liman kaura. Ya gabatar....

FASARAR HUDUBAR MASSALACIN JUMUAH NA UMAR IBN ABDILAZIZ ALBARKAWA GUSAU, TA RANAR JUMUAH 20/11/1447.9/5/2026D.TAKENTA SH...
09/05/2026

FASARAR HUDUBAR MASSALACIN JUMUAH NA UMAR IBN ABDILAZIZ ALBARKAWA GUSAU, TA RANAR JUMUAH 20/11/1447.9/5/2026D.
TAKENTA SHI NE:Riko da Alkura'ni.

Godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai Mai Rahma Mai jinkai mamallakin ranar sakamako,salati da Aminci ya tabbata ga Muhammad mahi hitan bayin Allah Kuma mahi darajar su Baki daya, da iyalansa da sahabbansa masu riko da Alkura'ni boyen su da bayyane su da Wanda yabi hanyar su har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka:Kuji tsoron Allah yaku bayin Allah,Ku kiyaye shi Kuma ku sani,shi Alkura'ni maganar Allah ne Wanda ya saukarda shi ga masoyinsa zababbensa mahihitan halittar Allah Baki daya, Muhammad Sallallahu Alaihi wasallam domin shiryarda halitta zuwa ga hanya mikakka, da abinda cikinsa akwai alkairin su da gyaruwar su cikin duniya da lahira.

Saboda kwadaitarwa akan yin Imani dashi da huskantarsa da bin umurnin sa da nisantar haninsa Allah ya yabesa, shi maganarsa ne Kuma sifane daga sifofinsa,yana daga cikin yabonda yayi masa cewa" Wannan Alkura'ni yana shiryarwa zuwa ga hanya mahi dai daita, wato Hanyoyi da halayae da sunnoni wadda itace mahi dai daituwar Hanyoyi, Alkura'ni yayi kira zuwa ga dukkan littahwan da aka saukar daga sama, waje sura ta hanyar lura. da daukakarsa da bayaninsa,cikin alkawullansa ta hanyar lura da gamewarsa ga dukkan halittu cikin duniya da lahira,cikin asali Kuma ta hanyar juyaisalansa da tabbatarda Hanyoyi da yanke duk wata kamanceceniya da bayyanarda huskoki na dalilai.
Imamu katada yace"Wannan Alkura'nin yana shiryarda ku zuwa ga cutarku da Kuma warakar ku.

Kuma yana shiryarda Alumma ga akida wadda Babu Daure Kai cikinta da Kuma wahala, Kuma yana shiryarwa zuwa ga tsari mahi kyau tsakanin boyen mutum da Kuma bayyanen sa,tsakanin akidarsa da aikinsa.

Kuma yana shiryarwa zuwa ga hanya mahi dai daita cikin ibadah ta hanyar dai daitawa tsakanin aikin da aka dorawa mutum da Kuma iKon yin aikin, duk abinda Allah ya dorawa bayi ba Mai wahala bane suna iyashi.

Kuma ya shiryarwa zuwa ga hanya mahi kyau cikin alakokin mutane sashen su da sashe, dai daiku da Kuma hade hukumomi da alumma, Kuma yana tabbatarda ita wannan Alakar wadda son Rai baya tasiri cikinta ko raayi.

Shi Allah yasan wadanda ya halitta yasan abinda ya dace dasu cikin kowace kasa da kowace jamaah, Kuma yana shiryarwa zuwa ga jinginuwa zuwa ga Addinai na sama Baki dayan su da girmama wuraren Addinanta masu tsarki da kiyaye alhwarmarta,sai duk Alumma su kasance da duk akidun su su zamo cikin Aminci da hadinkai.
Wadanda basu shiriya da wanga Alkura'nin to zaa Bassu ga bin son Ran mutane,mutum Mai gaugawa Mai jahilci ga abinda zai cuta masa baya amfaninsa.

Kamar yadda yazo cikin Alkura'ni sifanta Alkura'ni da sifofi masu kyau Kuma ya kwadaitar akan riko dashi, haka yazo cikin wasiyoyin Annabi Sallallahu Alaihi wasallam riko da Alkura'ni, Muslim ya ruwaito Annabi Sallallahu Alaihi yace "Yaku mutane ni mutum ne irin ku ya kusa Dan sakon ubangijina yazomin sai in karba Kuma na bammuku abubuwa masu nauyi biyu daga cikin su littahin Allah cikin shi akwai shiriya da haske kuyi riko da littahin Allah ku kamashi ,ya kwadaitar akan riko da Alkura'ni sannan yace da iyalan gidana a Wani lafazin littahin Allah, shi igiyar Allah ne Mai karhi Wanda yabishi yana bisa hanya ta shiriya,Wanda ya basshi yana akan bata.

Tirmizi ya ruwaito Kuma yace hadisi ne garibi daga Aliyu Allah ya yarda dashi yace naji manzon Allah Sallallahu Alaihi wasallam yana cewa "Ku saurara Hitinar zata kasance sai nicce minene mahita daga gareta? Sai yace littahin Allah, cikin shi akwai labarin wadanda s**a gabace ku da labarin wadanda suke bayan ku shi Mai rabewa ne ba wasa bane duk Wanda ya basshi domin girmankai Allah zai kalleshi Wanda ya nemi shiriya daga waninsa Allah zai batarda shi, shi igiyar Allah ne Mai karhi Kuma ambato ne Mai kyau hanya ne mikakka...
Yaku bayin Allah duk abinda ya gangaro na kwadaitarwa akan riko da Alkura'ni to ana nuhin riko dashi hadeda Sunnah domin sune asalin shariah basu rabuwa.
Wassalamu Alaikum
Imam Bashir Siraj Gusau.

Address

Gusau

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ministry For Religious Affairs Zamfara State posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share