19/01/2026
Kisan da aka yiwa Mata da yaranta biyar a Kano laifinmu ne baki daya. A yau ba ina magana bane a matsayina na ɗan Kano ko dan Arewa. Ba ina magana bane a matsayin ɗan gwagwarmaya ba.
Kuma Ba ina magana a matsayin malami ko wani fitacce ba.
Ina magana ne a matsayin ɗan Adam wanda zuciyarsa ta shiga wani irin mugun hali sakamakon abin da ya faru. Mace guda. ’Ya’ya biyar. An yanka su. Ba daga wasu baƙi ba. Ba daga “aljanu” da aka sauko da su daga wani wuri ba. Sai dai samari da al’ummarmu da kanta ta haifa.
Wannan ba kisan kai kaɗai ba ne. Wannan madubi ne. Kuma abin da muke gani a cikin wannan madubi ya kamata ya fi mana tsoro fiye da jinin da ya zube.
Mu daina yaudarar kanmu. Wannan bala’i bai fara yau ba. Bai fara da miyagun ƙwayoyi ba. Bai fara da siyasa ba. Kuma Bai fara da addini ba. Ya fara ne ranar da muka yi sabo da lalacewar alummarmu. Ranar da muka ce: “Ba ruwana.”Ranar da muka ga yaro yana yawon dare, muka ce: “Allah zai kiyaye.”
Ranar da muka ga miyagun ƙwayoyi sun cika unguwanni, muka ce: “Ai gwamnati ce.”Ranar da muka daina koyar da ’ya’yanmu daidai da ba daidai ba, muka maye gurbinsa da tsoro, shiru, da biyayya kamar makafi.
Hakika, miyagun ƙwayoyi suna lalata matasanmu Amma waye ya raina waɗannan matasa? Wa ya bari tramadol ya fi gurasa araha? Wa ya bari codeine ya maye gurbin karatun islamiyya da boko? Wa ya kalli samari suna lalacewa cikin zaman banza, ya ce “ƙaddara ce”?
Muna zargin ƙwayoyi, amma muna ƙin yaƙar yanayin da ke sa su zama abin jan hankali:
1. Ilimi marar gina tunani.
2. Rashin aikinyi da rashin ganin matasa da mutunci.
3. Rashin makoma da ke haifar da takatsantsan.
Sannan Hakika, ilimi ya rushe. Amma waye ya kashe shi? Mun mayar da makarantu makabartu. Mun raina ilimi sai mai kawo kuɗi nan take.
Mun bar malamai cikin yunwa, mun ɗaukaka ’yan damfara. Mun haifi masu shaidar karatu da za su iya karantawa, amma ba za su iya tunani ba.
Masu tsoron gwamnati, amma marasa fahimtar alhaki.
Hakika, shugabanci ya gaza. Amma waye ke ci gaba da sake zaɓar masu laifi? Muna zagin shugabanni a ɓoye, amma muna kare su a fili saboda: “Namu ne”Addininsa ɗaya da namu. Yarenmu ɗaya. Muna yafewa sata, zalunci, da rashin cancanta muddan dai suna sanye da suna ko kaya irin namu.
Saboda haka meye abun mamaki idan al’umma ta zama babu doka? Ba za ka iya ɗaukaka cin hanci ba, sannan ka sa ran samun zaman lafiya. Ba zai taba yiwuwa ba. Amma ga gaskiyar da ta fi ciwo Mu talakawan nan muna da babban laifi.
Muna rainon yara ba tare da ladabtarwa ba. Muna tsoron gyara kuskure saboda “kar a ce ka tsoma baki.”Muna kare masu laifi saboda “ai ɗanmu ne.”Muna zagin al’umma, amma muna ƙin sadaukar da jin daɗinmu don gobenmu.
Muna jiran:
Gwamnati ta gyara ’ya’yanmu.
Malamai su gyara ɗabi’unmu
’Yan sanda su gyara lamirinmu.
Alhali muna zaune lafiya, muna kallon lalacewa na yaɗuwa kamar wuta.
An maida addini makami. Ba domin gina ɗabi’a ba, amma domin boyewa daga tambayoyin s**a dace mu amsa.
Muna ambaton addini idan ya dace da mu,
muna watsi da shi idan ya buƙaci ladabi, tausayi, adalci, da kamun kai. Addini ba tare da ɗabi’a ba ihu ne kawai. Imani ba tare da alhaki ba munafunci ne.
Allah ba ya karɓar hujjar zubar da jini.
Kabilanci ya zama mafaka. Duk lokacin da laifi ya faru, sai mu tambaya: “Su wane ne? “ Maimakon mu tambaya: “Wace irin al’umma ce ta haifi wannan?” Mugunta ba ta da kabila.
Sakaci ne ke haifar da ita.
Abin da ya faru a Kano ba keɓantacce ba ne Gargaɗi ne.
Idan muka ci gaba haka:
Allah Ya kiyaye amma za a samu karin yara da za su mutu
Ƙarin mata za a binne
Ƙarin matasa za su koma dodanni.
Mu kuma mu ci gaba da yin mamaki. Har wata rana, ƙofar namu gidan ne za a balla a shigo.
Don haka ina tambayar ku, mutanenmu.
Yaushe za mu karɓi alhaki?
Yaushe iyaye za su koma iyaye?
Yaushe dattawa za su koma jagorori
Yaushe al’umma za ta zana jan layi?
Yaushe za mu daina mika lamiri ga wasu?
Babu wata gwamnati da za ta ceci al’umma da ta ƙi ceton kanta.
Jama’a Rokonku nake. Daga zuciyata come da bakin ciki. Daga wanda ke cike da takaici.
Daga wanda har yanzu yake ganin canji na yiwuwa idan muka yi ƙarfin hali baki dayanmu. Muna jimamin wadanda s**a rasu, amma dole sai mun dena yi wa kanmu ƙarya.
Domin idan ba mu yi haka ba, ƙarin kaburbura suna jiranmu. Kuma tarihi ba zai gafarta mana ba saboda mun yi shiru, alhali muna sane. A cikin comment ka rubuta