22/07/2026
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa Jihar Kano ta shirya tsaf domin kafa Rundunar ’Yan Sandan Jiha, yana mai cewa wannan tsari zai taimaka wajen ƙarfafa tsaron cikin gida, bunƙasa aikin tsaron al’umma, da kuma kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin ƙaddamar da Kwamitin Haɗin Gwiwa na Hukumomi Kan Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi da Fataucinsu, a ɗakin taro na Gidan Gwamnatin Jihar Kano.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Darakta Janar na Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Gidan Gwamnatin Jihar Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Laraba.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce Rundunar ’Yan Sandan Jiha da ake shirin kafawa ba za ta maye gurbin Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya ba, kuma ba za ta yi gogayya da ita ba. Ya ce manufar ita ce ta ƙara wa aikin rundunar ƙarfi, domin dukkansu suna da nauyin kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tabbatar da doka da oda, da kuma inganta zaman lafiya.
Ya ƙara da cewa rundunonin biyu za su yi aiki kafad