14/01/2023
HUKUMAR ZAKKA TA KANO TA SAMU ƘARIN HUBUSI.
Hukumar Zakka da hubusi ta jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Shugaban hukumar Farfesa Ibrahim Muazzam Mai bushira ya jagoranci jami'an hukumar wajen duba wani hubusi na gida da wani bawan Allah da ya rasu ya bar wasiyya domin barinsa a matsayin hubusi ƙarƙashin hukumar ta zakka.
A yayin wannan ziyara ta gani da ido, Farfesa Mai Bushra yana tare da Kwamishinonin hukumar da Daraktocinsa da kuma sauran ma'aikata. Inda s**a duba wannan gida domin ganin yadda yake tare da tsara abin da ya dace a yi da shi.
A ƙarshe an yi addu'a ga wannan mamaci bisa ga wannan aikin alkhairi da ya bayar da wasiccin a yi da dukiyarsa.