Arewa online news

Arewa online news Domin samun sahihan labarai Ku Cigaba da kasancewa da Arewa online news

NDC ta tantance Obi a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa daya tilo na jam'iyyar Kwamitin tantance ‘yan takarar shugaban ...
20/05/2026

NDC ta tantance Obi a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa daya tilo na jam'iyyar

Kwamitin tantance ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ya amince da Peter Obi a matsayin dan takarar shugaban kasa guda daya tilo kafin zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Obi ya isa hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja da misalin karfe 6:45 na yammacin ranar Talata tare da rakiyar Sanata Victor Umeh.

Tsohon gwamnan jihar Anambra ya gurfana a gaban kwamitin tantancewar karkashin jagorancin tsohon ministan ilimi, Sam Egwu.

Da yake magana bayan tantancewar, Egwu ya ce kwamitin ya gamsu da yadda Obi ya amsa tambayoyin da aka yi masa, yana mai cewa ya cika dukkan sharuddan kundin tsarin mulkin Najeriya da dokar zabe.

A cewarsa, kwamitin ya tabbatar da Obi a matsayin wanda ya cancanci shiga zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar domin zaben shekarar 2027.

Daga nan ne aka mika wa Obi takardar shaidar amincewa tare da fom din tsayawa takara mai lamba 001 na jam’iyyar.

A ranar Lahadi 17 ga watan Mayu ne Obi ya karbi fom din nuna sha’awa da na takarar shugaban kasa na jam’iyyar NDC kafin wa’adin farko da aka sanya.

Sai dai a ranar Litinin jam’iyyar ta kara wa’adin karbar fom ga sauran masu neman takara zuwa ranar 24 ga watan Mayu, tare da bayyana cewa karbar cikakkun fom daga wadanda aka tantance zai fara daga ranar 20 zuwa 26 ga watan Mayu.

Duk da haka, jam’iyyar ta ce ba za a kara wa’adin karbar fom din takarar shugaban kasa ba domin tuni an rufe shi.

Da ɗumi-ɗumi: Kwankwaso Ya Ce Kujerar Mataimakin Shugaban Ƙasa A NDC Za Ta Buɗe Wa Kano Hanyar Samar da Shugaba ƙasa Jig...
19/05/2026

Da ɗumi-ɗumi: Kwankwaso Ya Ce Kujerar Mataimakin Shugaban Ƙasa A NDC Za Ta Buɗe Wa Kano Hanyar Samar da Shugaba ƙasa

Jigo a jam’iyyar Nigeria Democratic Congress, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa yana da kwarin gwiwar samun tikitin takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar, yana mai cewa hakan zai buɗe wa jihar Kano State ƙofa domin samar da shugaban ƙasa a nan gaba.

Kwankwaso ya ce idan har sunan sa ya bayyana a takardar zaɓe a babban zaɓen gaba, to za a ga wani irin sauyi da ba a taɓa gani ba a jihar Kano da ma ƙasar baki ɗaya.

“Da yardar Allah, zaɓen gaba zai bambanta da duk wani zaɓe da aka taɓa yi a jiharmu da ƙasarmu, musamman idan na samu tikitin takara kuma sunana ya kasance a kan takardar zaɓe,” in ji Kwankwaso.

Kalaman nasa na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tattaunawa da hasashen siyasar 2027 a faɗin Najeriya, inda manyan jam’iyyu da ’yan siyasa ke ci gaba da shirye-shiryen tunkarar babban zaɓen ƙasa.

Masu bibiyar siyasa na ganin furucin Kwankwaso na iya ƙara ɗaga zafin siyasar Arewa musamman a jihar Kano, wadda ta kasance ɗaya daga cikin jihohin da ke da yawan masu kaɗa ƙuri’a a Najeriya.

Duk da ya na da fayil a EFCC, Yahaya Bello ya samu tikitin takarar Sanata a KogiTsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello,...
19/05/2026

Duk da ya na da fayil a EFCC, Yahaya Bello ya samu tikitin takarar Sanata a Kogi

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar APC domin takarar Sanatan Kogi ta Tsakiya, duk kuwa da yana da fayil a hukumar EFCC.

Jami’in tattara sakamakon zaben, Dr. Sadiq Mohammed, ne ya sanar da hakan a ranar Litinin, inda ya ce tsohon gwamnan ya samu kuri’u 72,349, lamarin da ya ba shi nasara a kan abokan hamayyarsa mafi kusa, Ibrahim Yakubu Adoke wanda ya samu kuri’u 315 da kuma Momoh Yusuf Obaro da ya samu kuri’u 188.

A yankin Sanatan Kogi ta Yamma kuwa, rahotanni sun nuna cewa Sanata mai ci, Sunday Karimi, na kan gaba yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben.

Hakan ya biyo bayan janyewar wasu manyan masu neman tikitin takarar, ciki har da Sanata Smart Adeyemi da Samuel Bamidele Aro, gabanin kammala zaben, lamarin da ya kara bai wa Sunday Karimi damar samun nasara.

A Kogi ta Gabas kuma, rahotanni sun nuna cewa Sanata mai ci, Jibrin Isah Echocho, na baya a sakamakon da aka fitar kawo yanzu.

An ce ya sha kaye a karamar hukumarsa ta Dekina inda ya samu kuri’u biyu kacal, yayin da babban abokin hamayyarsa, Dr. Joe Erico Ameh, ya samu kuri’u 19,805.

Majiyoyin jam’iyyar sun bayyana Dr. Joe Erico a matsayin dan takarar da manyan masu ruwa da tsaki a jihar ke goyon baya.

A halin da ake ciki, wasu daga cikin manyan ‘yan takarar da s**a hada da Muritala Ajaka da Jibrin Echocho sun soki yadda aka gudanar da zaben fidda gwanin, suna masu cewa bai bi ka’idoji da tsarin jam’iyyar yadda ya kamata ba.

DA ƊUMI-ƊUMI: Dandazon magoya bayan Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso a gidansa da ke Miller Road, yayin da ake shirye-shiryen...
30/03/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Dandazon magoya bayan Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso a gidansa da ke Miller Road, yayin da ake shirye-shiryen komawarsa jam’iyyar ADC a yau.

2027: Idan Atiku ya zabi Peter Obi a matsayin abokin takara, zai iya rasa kuri’un Adamawa — OmokriJakadan Najeriya da ak...
16/03/2026

2027: Idan Atiku ya zabi Peter Obi a matsayin abokin takara, zai iya rasa kuri’un Adamawa — Omokri

Jakadan Najeriya da aka nada zuwa kasar Mexico, Reno Omokri, ya gargadi tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, cewa zai iya fuskantar rasa goyon bayan siyasa a jiharsa ta haihuwa ta Adamawa idan ya zabi tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2027.

Omokri ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin, yayin da yake mayar da martani ga kalaman, Dele Momodu.

Rahotanni sun nuna cewa Momodu, yayin da yake bayani a shirin Sunday Politics na gidan talabijin na Channels, ya ce hadakar tikitin takara na Atiku da Obi za ta iya kayar da Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, a zaben shugaban kasa mai zuwa.

Sai dai Omokri, duk da cewa ya ce yana girmama Atiku, ya bayyana cewa zabar Obi a matsayin mataimakin takara na iya janyo Atiku ya rasa goyon bayan masu kada kuri’a a Arewacin Najeriya, inda ya ce addini da kuma abubuwan da s**a faru a tarihi kan yi tasiri wajen yanke shawarar siyasa.

Ya kuma yi ikirarin cewa har yanzu wasu mazauna Adamawa na ci gaba da nuna bacin rai kan yadda Peter Obi ya mayar da martani game da kisan Ahmed Gulak da aka yi a Owerri a shekarar 2021.

An harbe Gulak, wanda dan asalin Adamawa ne, har lahira ne daga wasu ‘yan bindiga a shekarar 2021.

A cewar Omokri, lamarin ya kara tsananta ne sakamakon yadda Peter Obi ya mayar da martani kan kisan wata mata mai juna biyu, Harira Jubril, da ‘ya’yanta, wanda ya faru a Anambra a watan Mayun shekarar 2022.

Siyasa ce ta sa aka rushe ma’aikatar ilimi mai zurfi a Kano - KwankwasiyyaKungiyar Kwankwasiyya Movement ta ce matakin d...
16/03/2026

Siyasa ce ta sa aka rushe ma’aikatar ilimi mai zurfi a Kano - Kwankwasiyya

Kungiyar Kwankwasiyya Movement ta ce matakin da gwamnatin Kano ta dauka na rushe ma’aikatar ilimi mai zurfi tare da hada ta da Ma’aikatar Ilimi yana da nasaba da siyasa.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin a Kano, mai magana da yawun kungiyar, Habibu Sale Mohammed, ya ce dalilin da gwamnati ta bayar na cewa ana yin gyaran tsarin gudanarwa bai bayyana hakikanin dalilin da ya sa aka dauki wannan mataki ba.

Ya ce rushe ma’aikatar da sunan sake fasalin tsarin gwamnati ya jawo damuwa kan fifikon gwamnati da kuma yadda take da niyyar gudanar da mulki yadda ya kamata.

Mohammed ya kuma zargi cewa matakin na iya kasancewa yana da alaka da halin siyasar da ya shafi mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwarzo, wanda ke kula da ma’aikatar kafin daukar wannan mataki.

A cewarsa, ana iya fassara matakin a matsayin yunkurin hukunta mataimakin gwamnan saboda kin barin kungiyar Kwankwasiyya.

Mai magana da yawun ƙungiyar ya kuma bayyana cewa tun a shekarar da ta gabata ma’aikatar ta riga ta raunana sakamakon wasu umarnin gudanarwa da s**a mayar da wasu daga cikin ayyukanta da hukumominta su rika kai rahoto kai tsaye ga gwamna.

Ya ce idan har akwai matsala kan wanda ya kamata ya kula da ma’aikatar, gwamnan zai iya sauya wanda ke rike da mukamin maimakon rushe ma’aikatar gaba daya, wadda ya bayyana a matsayin ma’aikata mai muhimmanci ga jihar.

An dakatar da mai horas da Man City, Guardiola wasanni biyuHukumar gasar Firimiya ta kasar Ingila ta dakatar da mai hora...
08/03/2026

An dakatar da mai horas da Man City, Guardiola wasanni biyu

Hukumar gasar Firimiya ta kasar Ingila ta dakatar da mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, Pep Guardiola daga buga wasanni biyu.

Wasannin da Guardiola na zai ja ragamar Man City sun hada da wasan da za.su buga da West Ham United a gasar Firimiya da kuma wasan zagayen na kusa da na karshe na gasar FA Cup da zasu buga a watan Afirilu.


Hakan ya biyo bayan katin kora da ya samu a wasan da Manchester City ta doke Newcastle United da ci 3-1 a gasar cin kofin FA a jiya Asabar

Ramadan: Gwamna Abba Gida Gida ya ƙaddamar da rabon buhunan shinkafa 100,000 na gidauniyar DangoteGwamnan Jihar Kano, Ab...
08/03/2026

Ramadan: Gwamna Abba Gida Gida ya ƙaddamar da rabon buhunan shinkafa 100,000 na gidauniyar Dangote

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da rabon buhunan shinkafa 100,000 da gidauniyar Aliko Dangote ta bayar domin tallafa wa marasa karfi a jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Mustapha Muhammad, ya fitar a Kano, gwamnan ya gode wa gidauniyar bisa wannan tallafi, yana mai cewa ya zo a daidai lokaci musamman a watan Ramadan.

Yusuf ya tabbatar da cewa za a raba tallafin cikin gaskiya da adalci ta hanyar shugabannin al’umma da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da cewa ya kai ga waɗanda aka nufa da shi.

Shi ma kwamishinan noma da albarkatun ƙasa na jihar, Dakta Danjuma Mahmud, ya yaba wa gidauniyar Dangote kan ba gwamnatin jihar damar kula da rabon tallafin kai tsaye.

Matashi daga jihar Kano ya ƙaddamar da takarar kujerar shugaban matasa na jam'iyyar APC na ƙasaWani dan jam’iyyar APC, B...
08/03/2026

Matashi daga jihar Kano ya ƙaddamar da takarar kujerar shugaban matasa na jam'iyyar APC na ƙasa

Wani dan jam’iyyar APC, Bashir Suwaid, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Shugaban Matasan jam’iyyar na kasa.

Suwaid, wanda dan asalin jihar Kano ne, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, inda ya ce ya dauki matakin ne bayan tuntuba da shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki na matasa a fadin kasar.

Da yake jawabi ga shugabannin jam’iyya da ‘yan jarida, Suwaid ya ce ya zama dole a kara karfafa bangaren matasan APC tare da inganta tsarinsa domin amfani da karfi da gudunmawar matasa a duk fadin kasar.

Ya ce matasan jam’iyyar sun taka muhimmiyar rawa wajen tattara goyon baya da kuma karfafa tsarin jam’iyyar tun daga matakin mazabu har zuwa kasa baki daya.

Suwaid ya kuma jaddada cewa matasan Nijeriya a yanzu sun fi ilimi da hadin kai, kuma suna da sha’awar ba da gudunmawa ga ci gaban kasa.

Ya kara da cewa ya shiga takarar ne cikin kaskantar da kai tare da girmama sauran masu neman kujerar, yana mai alkawarin yi wa jam’iyyar aiki da gaskiya idan aka ba shi dama.

A cewarsa, da goyon bayan shugabannin jam’iyya da matasa a fadin kasa, bangaren matasan APC zai kara karfi da hadin kai gabanin zabukan siyasa masu zuwa.

Kamfanonin rarraba wutar lantarki a Najeriya sun karɓi Naira biliyan 207.49 daga hannun Kwastomomi a watan Disambar shek...
08/03/2026

Kamfanonin rarraba wutar lantarki a Najeriya sun karɓi Naira biliyan 207.49 daga hannun Kwastomomi a watan Disambar shekarar 2025.

Na wa kuke biya duk wata?

Address

Audu Bako Secretariat
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa online news posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share