23/05/2026
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo, ya kada kuri’arsa a zaɓen fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar All Progressives Congress da aka gudanar a mazabarsa da ke Garo, Ƙaramar Hukumar Kabo.
Bayan kada kuri’ar, Garo ya yaba da yadda aka gudanar da zaɓen cikin lumana da tsari, yana mai bayyana cewa hakan na nuna jajircewar jam’iyyar wajen tabbatar da dimokuraɗiyya ta cikin gida da kuma bai wa talakawa damar shiga harkar siyasa kai tsaye.
Ya kuma jinjinawa jama’ar yankin—daga dattawa, mata zuwa matasa—kan fitowa kwansu da kwarkwata domin yin zaɓe cikin tsari da bin ƙa’idoji.
Wakilin jam’iyya a mazabar, Hon. Abba Salisu Me Wake, ya bayyana cewa sama da ƙuri’u 770 ne aka kaɗa, inda aka tabbatar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen a mazabar.
Ya yi addu’ar samun nasara ga jam’iyyar a gaba, tare da fatan ci gaba da samun nasarorin ci gaban ƙasa gabanin zaɓen 2027.