24/08/2026
Da ɗumi-ɗumi: “Na taɓa cire gwamna kan zargin sace Naira dubu ɗari uku N300,000, amma A yau Naira Biliyan dari uku N300bn ba ta isa dalilin cire gwamna ba a Najeriya” — IBB
Tsohon shugaban ƙasar Najeriya na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya bayyana cewa a lokacin mulkinsa ba a yi mulkin da cin hanci da rashawa ba, yana mai cewa yana alfahari da irin matakan da gwamnatinsa ta ɗauka kan almundahana.
A cikin kalamansa, Babangida ya ce:
“Mu ba ’yan cin hanci da rashawa ba ne. Ina alfahari da faɗin haka, domin ni ko yaushe ina karatun jarida. Duk abin da na gani a jarida, idan gaskiya ne, zan ɗauki mataki.”
Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin abubuwan da yake alfahari da su shi ne yadda gwamnatinsa ta ɗauki matakin ladabtar da jami’an gwamnati kan ƙananan zarge-zargen almundahana.
A cewarsa, ya taɓa cire wani gwamna daga mukaminsa saboda zargin satar Naira dubu ɗari uku (N300,000).
Sai dai Babangida ya bayyana abin da ya kira babban sauyi a yadda ake kallon almundahana a yau, yana cewa:
“Amma yanzu Biliyan ɗari uku (N300bn) ba ta isa dalilin cire gwamna ba.”
Kalaman na Babangida sun sake buɗe batun yadda ake yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya da kuma irin matakin da ya kamata a ɗauka kan jami’an gwamnati idan aka samu zargin almundahana.