31/03/2026
MATASA DAGA MAZABU UKU A FAGGE SUN BARRANTA KANSU GA SIYASAR BANGARANCI TARE DA TABA MUHIBBAR MANYAN MUTANE DA WASU MARASA TARBIYYA SUKAI...
A yammacin yau lahadi (29/03/2026) matasa daga mazabun Kwachiri, Rijiyar Lemo da Yammata Gabas, sun yi gagarumin taro domin barranta kansu da taron da waɗansu marasa tarbiyya su kai kwana biyu baya, wanda ke alaƙanta su da siyasar bangaranci tare da cin zarafi da wani da ake kira Isyaku Mai Fenti yayi ga Shehun Malami Farfesa Umar Sani Fagge.
Matasan da sukai taron a yau sun yi Allah wadai da wannan rashin tarbiyya tare da yin kira ga jami'an tsaro akan su tabbatar wancan mutum da yayi cin mutunci ya girbi abinda ya shuka, saboda abinda yayi ka iya zama barazana ga zaman lafiya ko kuma haddasa rikici a tsakanin al'umma.
A ƙarshe matasan sun jaddada goyon bayansu ga wakilin al'ummar ƙaramar hukumar Fagge a zauren majalisar ƙasa, Hon. (Barr.) Muhammad Bello Shehu ɗan majalisar dokokin jihar Kano mai wakiltar Fagge Hon. Muhammad Muhammad Tukur da shugaban ƙaramar hukumar Fagge Hon. Salisu Masu tare da bayyana cewa ƙaramar hukumar Fagge guda ɗaya ce.
Muna addu'a Allah Ubangiji ya cigaba da ciyar da wannan ƙaramar hukuma gaba, kana yayi riƙo da hannun shugabanninta, ya kuma bamu zaman lafiya da arziƙi mai ɗorewa, ameen.
29/03/2026