18/05/2026
Minista Darma Ya Tallafawa Dalibai 33 Kudin Rubuta Jarabawar NECO a Katsina
Ministan Gidaje da Raya Birane na Tarayya, Injiniya Muttaqha Rabe Darma, ya bayar da tallafin sama da Naira Miliyan ɗaya (1,072,000) domin biya wa dalibai 33 kudin rubuta jarabawar NECO a jihar Katsina.
An mika tallafin ne ta hannun mataimakin Ministan na musamman, Alhaji Gambo Garba, yayin wata ziyara da tawagarsa ta kai makarantar mata ta WTC da ke Katsina domin ganawa da shugabar makarantar, Hajiya Hadiza Nasir.
A cewar Gambo Garba, Ministan ya amince da bayar da tallafin ne bayan samun roko daga makarantar dangane da halin da wasu daga cikin daliban ke ciki, musamman marasa galihu da marayu da ke fuskantar barazanar rasa damar ci gaba da karatu.
Ya bayyana cewa Injiniya Darma na daga cikin masu bai wa harkar ilimi muhimmanci, yana mai ganin cewa ilimi shi ne ginshikin ci gaban al’umma da makomar matasa.
Da take jawabi bayan karbar tallafin, shugabar makarantar ta nuna godiyarta ga Ministan, tana mai cewa duk da ta nemi taimako daga mutane da dama, Injiniya Muttaqha Rabe Darma ne kadai ya amsa koken daliban tare da daukar nauyin kudin jarabawar nasu.