Adon Garin Katsina Mobile Media

Adon Garin Katsina Mobile Media experience in political communication, campaign messaging, and social media engagement. I create enga

Jagoranmu, Hon. Dr. Musa Lawal Jibia, PhD, FNIM, Adon Garin Katsina, ɗan takarar Majalisar Tarayya a Jam'iyyar ADC, tare...
19/07/2026

Jagoranmu, Hon. Dr. Musa Lawal Jibia, PhD, FNIM, Adon Garin Katsina, ɗan takarar Majalisar Tarayya a Jam'iyyar ADC, tare da mai girma ɗan takarar Gwamnan Jihar Katsina na Jam'iyyar ADC, Distinguished SEN. Ahmad Babba Kaita sun halarci jana'izar marigayi Magaji Sauri, mahaifin Alhaji Ali Isa Girka, a garin Girka da ke Ƙaramar Hukumar Kaita.

Haka kuma Mahaifi ga Hon. Shamsu Abdallawa, ɗan takarar Majalisar Jiha na Ƙaramar Hukumar Kaita a Jam'iyyar ADC, ya kasance cikin tawagar.

A yayin ta'aziyyar, Hon. Dr. Musa Lawal Jibia ya bayyana cewa rasuwar Marigayi Magaji Sauri ba rashi ba ne ga al'ummar Girka ko Ƙaramar Hukumar Kaita kaɗai, illa rashi ne da ya shafi ɗaukacin al'ummar Jihar Katsina har ma da ƙasar Hausa baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa, kasancewar marigayin mai riƙe da sarauta ne a masarautarmu ta gargajiya, ya bar kyakkyawan tarihi na shugabanci da gudanar da mulki cikin adalci, abin da al'umma da dama s**a shaida.

Muna addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa, Ya yalwata masa rahama, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa, Ya kuma bai wa iyalansa da ɗaukacin al'umma haƙurin jure wannan babban rashi. Ameen.

Maigirma Jagora, Hon. Dr.  Musa Lawal Jibia PhD, FNIM, Adon Garin Katsina, ɗan takarar Majalisar Tarayya mai wakiltar Ka...
11/07/2026

Maigirma Jagora, Hon. Dr. Musa Lawal Jibia PhD, FNIM, Adon Garin Katsina, ɗan takarar Majalisar Tarayya mai wakiltar Kaita/Jibia a ƙarƙashin Jam'iyyar ADC, ya kai ziyarar ta'aziyya a garin Dank**a.

Jagoran ya ziyarci gidan tsohon ɗan takarar Majalisar Jiha na Ƙaramar Hukumar Kaita a Jam'iyyar ADC, Hon. Sahibu Yusuf Dank**a, domin miƙa ta'aziyyar rasuwar ƙanen mahaifinsa.

Daga bisani kuma, Jagoran ya kai ziyara zuwa Masarautar Dank**a, inda ya miƙa ta'aziyyarsa tare da gaisuwa, sannan ya sake jaddada biyayyarsa ga iyayenmu Sarakunan Gargajiya.

Wannan ziyara ta sake nuna irin ɗa'a, ladabi, girmama al'ada, da kuma mutunta sarakunan gargajiya da Jagora Hon. Dr. Musa Lawal Jibia ke da shi.

Allah Ya jiƙan mamacin da rahama, Ya gafarta masa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa. Allah Ya ba iyalai da al'ummar Dank**a haƙurin jure wannan babban rashi. Amin.

Aminu Abubakar Kaita ✍️

Hon. Sada Soli ya gaza wajen cika wasu daga cikin manyan abubuwan da al'umma ke sa ran wakilinsu zai yi. A lokuta da dam...
07/07/2026

Hon. Sada Soli ya gaza wajen cika wasu daga cikin manyan abubuwan da al'umma ke sa ran wakilinsu zai yi. A lokuta da dama, ba a cika ganin sa a ayyukan da s**a shafi ci gaban al'umma ko shirye-shiryen tallafawa jama'a ba.

Mutane da dama a mazabarsa na bayyana rashin gamsuwa da irin wakilcin da suke samu, kuma suna ganin ya k**ata a mayar da hankali wajen kawo ayyukan ci gaba da magance matsalolin al'umma maimakon siyasa kawai.

Idan akwai wani bayani ko hujja da ke nuna akasin haka, yana da kyau a fito da ita domin jama'a su yi hukunci bisa gaskiya da adalci.

An tsare Dr. Bishir Kurfi bayan zargin da ya yi cewa Gwamnatin Jihar Katsina ta biya wa wasu da ake zargi da aikata laif...
07/07/2026

An tsare Dr. Bishir Kurfi bayan zargin da ya yi cewa Gwamnatin Jihar Katsina ta biya wa wasu da ake zargi da aikata laifuka kuɗin aikin Hajji.

Idan hakan gaskiya ne, ya k**ata hukumomi su gudanar da bincike na gaskiya tare da bayyana sak**akon ga jama'a. Idan kuma zargin ba shi da tushe, ya k**ata a fayyace hakan ta hanyar hujjoji.

Kamun mutum saboda zargi kawai, ba tare da an bayyana cikakkun bayanai ba, na iya haifar da damuwa game da 'yancin faɗar albarkacin baki da kuma bin doka da oda. Muna kira ga hukumomin tsaro da su tabbatar an bi dukkan ka'idojin doka, tare da mutunta haƙƙin kowane ɗan ƙasa.

Haka kuma, ya dace Gwamnatin Jihar Katsina ta fito ta yi cikakken bayani kan zarge-zargen da ake ta yadawa domin kawar da shakku da tabbatar da gaskiya. Abin da jama'a ke buƙata shi ne gaskiya, adalci da kuma gaskiya ta fito fili.

Domin har yanzu Gwamnatin Jihar Nan Bata Yi bayanin komai ba bayan an k**a Yanta'adda 7 a yayin Dawowarsu Daga Saudiyya idan Babu Rami Miya kawo Rami saboda haka a gaggauta sakin Dr Bashir Nan take.

Hon. Dr. Musa Lawal Jibia PhD, FNIM – Adon Garin KatsinaKasancewar Hon. Dr. Musa Lawal Jibia gogaggen ɗan siyasa ne mai ...
07/07/2026

Hon. Dr. Musa Lawal Jibia PhD, FNIM – Adon Garin Katsina

Kasancewar Hon. Dr. Musa Lawal Jibia gogaggen ɗan siyasa ne mai nagarta, ƙwarewa da cancantar jagoranci, ya sa masu adawa da shi s**a rasa abin da za su soke shi da shi.

Abin da ake ji kawai suna faɗi shi ne wai ba shi ne ɗan takara ba, ko ba za a ga sunansa a shafin INEC ba, ko kuma ADC ba za ta kasance a takardar zaɓe ba. Bayan waɗannan maganganu, babu wani aibi da za su jingina masa.

Wannan abin godiya ne ga Allah, domin Ya azurta mu da jagora nagari mai tsafta da kyakkyawan tarihin siyasa. Abin da ya rage wa masu adawa shi ne tsoro, domin sun tabbatar cewa idan Hon. Dr. Musa Lawal Jibia ya tsaya takara, fafatawa da shi ba za ta kasance mai sauƙi ba.

Ko a cikin PDP ko APC, ana ganin suna ɗaukar takararsa da muhimmanci. Mu kuma muna gode wa Allah da wannan ni'ima da Ya yi wa jagoranmu.

Allah Ya ba shi nasara, Ya kuma ba shi ikon ci gaba da yi wa al'umma hidima.

Kai Tsaye Daga Birnin Tarayya Abuja A Yau 6/7/2026, inda Hukumar Zaɓe ta Ƙasa Mai Zaman Kanta wato Independent National ...
06/07/2026

Kai Tsaye Daga Birnin Tarayya Abuja A Yau 6/7/2026, inda Hukumar Zaɓe ta Ƙasa Mai Zaman Kanta wato Independent National Electoral Commission (INEC) ta miƙa Foam na Certificate na takarar Majalisar Tarayya ta Kaita/Jibia a ƙarƙashin Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ga Jagora Hon. Dr. Musa Lawal Jibia PhD, FNIM, Adon Garin Katsina.

A yayin wannan gagarumin taro, Jagoran ya gabatar da wasu muhimman jawabai masu cike da fata da hangen nesa ga al’ummar mazabar Kaita/Jibia da jihar Katsina baki ɗaya. Ya jaddada kudirinsa na kawo cigaba, gaskiya, da wakilci na gari idan Allah Ya ba da dama.

In Sha Allah, nan ba da jimawa ba Hukumar INEC za ta bayyana sunansa a shafinta na portal a hukumance, wanda hakan zai kawo ƙarshen duk wata jita-jita, ƙage ko kuma lalata da wasu ke ƙoƙarin yi dangane da takararsa.

Al’umma da magoya baya sun bayyana wannan rana a matsayin wata sabuwar alama ta nasara da ci gaba ga siyasar Kaita/Jibia da jihar Katsina baki ɗaya.

Tun da aka kafa Najeriya ban taba ganin gwamnatin da take raina hankalin al’umma k**ar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ba. A...
03/07/2026

Tun da aka kafa Najeriya ban taba ganin gwamnatin da take raina hankalin al’umma k**ar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ba. A kullum sai an fito da wani sabon labari domin a dauke hankalin jama’a daga matsalolin da suke addabar kasa.

Ta yaya za a ce mutum wai ba jami’in gwamnati ba ne, amma yana da ofis a babbar sakatariyar kasa, yana karbar bakuncin manyan baki daga cikin gwamnati da ma kasashen waje, ana daukar hotuna ana yadawa a kafafen sada zumunta ba sau daya ba, ba sau biyu ba, amma wai yanzu ne gwamnati ta gano cewa mutum din bogi ne?

Wannan magana ba ta daure kai ba ne kawai, rainin hankali ne karara ga ‘yan Najeriya. Domin babu yadda za a yi mutum ya kai wannan matsayi ba tare da akwai masu ba shi kariya da goyon baya daga cikin gwamnati ba.

Idan da gaske gwamnati ba ta san da shi ba, toh hakan yana nuna gazawa da rashin tsari a gwamnatin. Idan kuma tana sane, toh tana kokarin yaudarar jama’a ne domin ta wanke kanta daga abin da ya tonu.

Saboda haka, maimakon a fito ana surutai da yada bayanai masu rikitarwa, abin da ya dace shi ne a kai shi kotu cikin gaskiya da adalci domin ya gabatar da hujjojinsa. Amma ba a k**a mutum a dinga azabtar da shi kafin a tabbatar da laifinsa ba, domin kundin tsarin mulkin kasa ya bai wa kowa damar kare kansa a gaban kotu.

‘Yan Najeriya ba yara ba ne da za a dinga wasa da hankalinsu. Jama’a sun fara gane gaskiya kuma babu wani wasan kwaikwayo da zai iya boye gazawar gwamnati.

Kotu ta tabbatar da tsagin su David Mark a matsayin halastattun shugabannin ADCKotun Tarayya da ke Abuja ta tabbatar da ...
02/07/2026

Kotu ta tabbatar da tsagin su David Mark a matsayin halastattun shugabannin ADC

Kotun Tarayya da ke Abuja ta tabbatar da halaccin shugabancin Sanata David Mark a jam'iyyar ADC, bayan ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar tarayya Leke Abejide ya shigar yana ƙalubalantar shugabancin jam'iyyar.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito mai shari'a Musa Liman ne ya bayyana cewa ƙarar ba ta da ingantaccen tushe, tare da tabbatar da David Mark a matsayin shugaban jam'iyyar, sannan ya amince da Rauf Aregbesola a matsayin sakataren ƙasa na ADC.

01/07/2026

Ya Allah Kaimana Chanji Mafi Alkhairi

Address

Kaita LGA
Katsina
820103

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Adon Garin Katsina Mobile Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share