03/04/2026
Duk damar daya kamata mu bai wa Hon. Sada Soli mun riga mun ba shi.
Yau ba maganar jamâiyya ake yiba magana ake ta ci gaban Kaita da Jibia.
Tambaya ita ce: wace irin dama ce kuma ta rage da za mu sake ba shi?
Mun zabe shi karo na farko ya yi shekaru 4.
Ya sake dawowa ya yi wasu 4.
Ya kuma sake yin wani zangon shekaru 12 kenan a hannunsa.
Amma abin takaici, cikin wadannan shekaru 12, alamomin gazawa sun bayyana a fili.
Toh, wace irin uzuri ne ya rage da za mu kara ba shi?
Ai inaga ko gado yaci Kujerar Kaita Jibia ai yakamata ya sauka haka Nan a Baiwa Wani Shima muka irin tasa.
Idan muka ci gaba da rufe ido, muna ba shi uzuri, to lallai nan gaba kadan:
Ilimin mu zai kara tabarbarewa
Sanaâoâin mu za su rushe
Ci gaban mu zai tsaya cik
Za mu zama baya a kowace fuska.
Bugu da kari, za a kara yawaitar zaman banza, inda kowa zai dogara da sai anje wajen mutum daya a nema.
Har ila yau, ya zama kamar babu wanda zai iya yin wani abu a siyasance a Kaita da jibia sai da yardarsa wannan ba dimokuradiyya bace.
Saboda haka, domin kare makomar:
âyaâyanmu
kannanmu
da alâummar mu gaba daya
Ya zama wajibi mu tashi tsaye mu dauki mataki.
magana ake ta ceton alâumma.
Lokaci ya yi da za mu kubutar da Kaita da Jibia daga wannan yanayi.
Insha Allahu, a ranar zabe, kafin karfe 10 na safe, za mu yanke hukunci mu sallame shi ya dawo
Aminu Abubakar Kaita âď¸