05/01/2026
SANARWA DA SAƘON TA’AZIYYA
Hukumar wan nan makaranta na sanar da iyaye, ɗalibai, ma’aikata, da al’ummar gari baki ɗaya.
Makarantar na bin umarnin da Gwamnatin Jiha da Ƙaramar Hukumar Nguru s**a bayar dangane da mummunan lamari da ya faru jiya.
Bisa ga lokacin jimami da aka amince da shi, makarantar za ta kasance baza tayi aiki ba a yau da gobe. Duk harkokin karatu da na ofis za su ci gaba a ranar Laraba.
Wannan mataki na nuna girmamawa, juyayi, da cikakken bin umarnin hukumomi.
Malamai, da ɗaliban Makarantar Ammar Bin Yasir Islamic Academy. suna miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda s**a rasu. Muna taya ku jimami da alhini.
Muna roƙon Allah SWT Ya gafarta wa mamatan, Ya saka su a Aljannatul Firdausi, Ya ba iyalansu haƙuri da ƙarfin zuciya.
Muna kuma roƙon Allah Ya kare al’ummarmu daga aukuwar irin wannan masifa a gaba
Sa hannu,
Hukumar makaranta