DGL Hausa

DGL Hausa DGL Hausa – Duniyar Labarai kafar yada labarai ce ta zamani da ke kawo sahihai kuma ingantattun labarai cikin harshen Hausa.

Gwamnatin Jihar Sokoto ta amince da sayen nau'o'in taki, ingantattun irorin amfanin gona da magungunan noma da kudinsu y...
12/06/2026

Gwamnatin Jihar Sokoto ta amince da sayen nau'o'in taki, ingantattun irorin amfanin gona da magungunan noma da kudinsu ya kai Naira biliyan 1.652 domin ƙara wa kayan aikin noma da ƙananan hukumomin jihar s**a riga s**a samar wa manoma ƙarfi.

An bayyana hakan ne bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Jihar da aka gudanar ranar Alhamis a zauren majalisar da ke Gidan Gwamnatin Jihar Sokoto.

An bayyana cewa wannan mataki na sayen taki, ingantattun irori da magungunan noma na da nufin tabbatar da cewa manoma sun samu kayan aikin noman tun farkon damina domin su amfana da su yadda ya kamata a lokacin noman bana.

Har ila yau, Majalisar ta amince da sayen babura kirar Daylong guda 1,200 da kudinsu ya kai Naira biliyan 1.609. Za a bai wa ma'aikatan gwamnati baburan ne ta hanyar tsarin rance.

Wannan na daga cikin alkawarin da Gwamna Ahmed Aliyu ya yi wa ma'aikata yayin bikin ranar Ma'aikata ta bana a jihar.

Haka kuma, Majalisar ta amince da ɗaga darajar Asibitin Kula da Lafiya na Farko na Gagi zuwa Babban Asibiti (General Hospital) kan kudi Naira miliyan 592.1.

Majalisar ta kuma amince da gina Cibiyar Kula da Lafiya ta Farko a Majemar Korino da ke yankin Tudun Wada a Ƙaramar Hukumar Sokoto ta Kudu kan kudi Naira miliyan 143.4, tare da gina ginin gudanarwa a cibiyar lafiya da ke kan titin Kontagora kan kudi Naira miliyan 192.9.

Bugu da ƙari, an amince da aikin gaggawa na siminti da gyaran magudanan ruwa da bututun ruwa da s**a rushe a bayan hanyar Rima Radio/Tudun Wada, wanda kudinsa ya kai Naira miliyan 246.9.

Majalisar ta kuma amince da girkawa da kula da tsarin hasken filin jirgin sama (Airfield Ground Lighting – AGL) a Filin Jirgin Sama na Kasa da Kasa na Sultan Abubakar III da ke Sokoto, kan kudi Naira miliyan 113.4.

Source BBG Hausa

🚨 FACEBOOK DA INSTAGRAM SUN FUSKANCI MATSALA A DUNIYA BAKI ƊAYA!Miliyoyin masu amfani da Facebook da Instagram a sassa d...
12/06/2026

🚨 FACEBOOK DA INSTAGRAM SUN FUSKANCI MATSALA A DUNIYA BAKI ƊAYA!

Miliyoyin masu amfani da Facebook da Instagram a sassa daban-daban na duniya sun fuskanci matsala bayan an fitar da su daga asusunsu ba tare da sun yi hakan da kansu ba.

Lamarin ya haifar da ruɗani yayin da masu amfani da dama s**a kasa shiga asusunsu ko kuma s**a fuskanci matsalolin amfani da wasu daga cikin ayyukan manhajojin.

Ana ci gaba da sa ido kan lamarin domin samun ƙarin bayani kan musabbabin matsalar da kuma matakan da ake ɗauka domin dawo da ayyukan yadda ya kamata.

KU gaya mana cigaban da mulkin demokradiyya ya kawo a yankin ku cikin shekaru 27 ba tare da yanke wa ba.
12/06/2026

KU gaya mana cigaban da mulkin demokradiyya ya kawo a yankin ku cikin shekaru 27 ba tare da yanke wa ba.


Zanga-zanga ta ɓarke a Legas kan matsalar tsaro da tsadar rayuwa a Najeriya.Masu zanga-zangar sun fito kansu da kwarkwat...
12/06/2026

Zanga-zanga ta ɓarke a Legas kan matsalar tsaro da tsadar rayuwa a Najeriya.

Masu zanga-zangar sun fito kansu da kwarkwatarsu a titunan birnin su na kira ga gwamnatin Tinubu da ta samar da tsaro, albarkacin ranar dimokuraɗiyya da ake bikinta yau juma'a, 12 ga watan Yunin 2026.

An ga wasu daga cikin su na ɗauke da kwalaye masu rubuce-rubuce kala-kala.

Ƙaramin Ministan tsaro na Najeriya, Bello Muhammad Matawalle ya zargi ƴan adawar ƙasar da zuzuta matsalar tsaro domin ɓa...
11/06/2026

Ƙaramin Ministan tsaro na Najeriya, Bello Muhammad Matawalle ya zargi ƴan adawar ƙasar da zuzuta matsalar tsaro domin ɓata sunan shugaba Bola Tinubu.

Matawalle ya yi zargin cewa suna yaɗa farfaganda domin cimma wata manufar siyasa da kauda hankalin mutane kan ci gaban da ake samu a ƙasar.

Ya ce ana samun nasarori sosai a yaƙi da matsalar tsaro da dakarun Najeriya ke yi musamman a yankin arewacin maso yammacin ƙasar.

"Babu wata farfaganda ko yarfen siyasa da za su kauda hankalin shugaban ƙasa kan cika alƙawuran da ya yi wa ƴan Najeriya," in ji shi.

Wata sanarwa da mai taimaka wa Ministan kan harkokin yaɗa labarai, Ahmad Dan-Wudil ya fitar, ta ambato Matawalle na cewa "duk da irin waɗannan s**a da ake yi, Tinubu na da farin jini a arewacin ƙasar."

Ministan ya ce Tinubu ne zai lashe zaɓen 2027 musamman a arewacin ƙasar saboda suna ganin irin nasarorin da ake samu.

"Ƴan adawar suna ganin irin ci gaban da ake samu a yaƙi da matsalar tsaro a faɗin ƙasar, sai dai su yaɗa farfaganda kawai" in ji Matawalle.

Ya ce gwamnatin Tinubu ta ƙara ƙaimi wajen yaƙar ƴan bindiga a jiihohin Sokoto, Zamfara, Katsina, Kaduna da Kebbi, kuma ana ganin sakamako mai kyau.

"Al'ummar yankin suna ganin irin ƙoƙarin da ake yi... muna da tabbacin cewa ƴan Najeriya na goyon bayan sauye-sauyen da ake samu".

Karanta wannan - Me ya sa matsalar tsaron Najeriya ta ƙi ƙarewa duk da kuɗin da gwamnati ke kashewa?

An buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan jinya da ungozoma a jihar Zamfara Hukumar bunƙasa fasahar zamani ta jihar Zamfara (ZITD...
11/06/2026

An buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan jinya da ungozoma a jihar Zamfara

Hukumar bunƙasa fasahar zamani ta jihar Zamfara (ZITDA) na sanar da al’umma cewa an buɗe shafin yanar gizo na ɗaukar ma’aikatan jinya (Nursing) da ungozoma (Midwifery), kuma yanzu haka masu neman aikin da s**a cancanta kuma ’yan asalin jihar ne za su iya neman aikin.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta nuna cewa za a rufe damar neman aiki ne a ranar 22 ga Yunin 2026, da misalin karfe 12 na dare.

Haka kuma, ta bukaci masu sha’awar neman aikin da su cika fom ɗin neman aikin ta wannan shafi👇
(https://recruitment.zamfara.gov.ng/HSMB/Apply)

tare da tabbatar da cewa sun cika dukkan sharuɗɗa da ƙa’idoji da aka gindaya.

HOTUNA: Yadda aka maida kabarin Sheikh Dahiru Usman Bauchi
11/06/2026

HOTUNA: Yadda aka maida kabarin Sheikh Dahiru Usman Bauchi

BADAKALA: Majalisar Dattawa ta bada umarnin kamawa da kawo mata tsohon shugaban Kamfanin NNPCL Mele Kyari a raye ko a ma...
10/06/2026

BADAKALA: Majalisar Dattawa ta bada umarnin kamawa da kawo mata tsohon shugaban Kamfanin NNPCL Mele Kyari a raye ko a mace bisa zargin almundahana da zunzurutun kudi har Nair Tiriliyon 210 daga shekarun 2017 - 2024.

Me zaku ce?

Address

No. 45 Tudun Wada Kaduna
Sokoto
58973

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DGL Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to DGL Hausa:

Share