30/07/2026
Gwamna Bago Ya Yabawa Ɗangote Kan Bunƙasa Harkokin Masana'antu a Nijeriya da Afrika
Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya yaba wa Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote kuma fitaccen attajirin Afrika, Alhaji Aliko Dangote, bisa jajircewarsa wajen bunƙasa ƙwarewa da bai wa al'umma damar ci gaba tun daga matakin ƙasa.
Gwamnan ya yi wannan yabo ne yayin wata ziyarar aiki da ya kai matatar mai da masana'antar sinadarai ta Dangote da ke Lekki a Jihar Legas.
A lokacin ziyarar, Gwamna Umaru Bago tare da Ƙaramin Ministan Masana'antu, Sanata John Owan Enoh, sun samu tarba daga Shugaban kuma Babban Daraktan Rukunin Kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote.
Gwamnan ya bayyana Aliko Dangote a matsayin jagora kuma abin koyi da ya samar wa 'yan Najeriya, musamman matasa, damar haɓaka basira da ƙwarewarsu.
Ya ce matatar mai ta Dangote ta zama wata muhimmiyar cibiyar koyon ilimi da ƙwarewa ga 'yan Afirka a fannin masana'antar man fetur da sinadarai. Ya kuma yaba wa Aliko Dangote kan wannan gagarumin aiki, wanda ya ce ya ɗaga martabar Najeriya da nahiyar Afirka a idon duniya.
A nasa jawabin, Alhaji Aliko Dangote ya gode wa Gwamna Umaru Bago bisa ziyarar da ya kai masa, sannan ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ƙara bai wa masu zuba jari na cikin gida cikakken goyon baya, yana mai cewa su ne za su taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasa.
Dangote ya ƙara da cewa samar da yanayi mai kyau ga masu zuba jari na cikin gida zai kuma ƙara jawo hankalin masu zuba jari daga ƙasashen waje.
Daga bisani, Aliko Dangote ya zagaya da gwamnan da tawagarsa domin duba manyan cibiyoyin masana'antu na zamani da ke cikin matatar mai.
Cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labaran gwamnan Ibrahim Bologi ya fitar, ta ce wannan ziyara ta nuna ƙudirin Gwamnatin Jihar Neja na ƙarfafa haɗin gwiwa da manyan kamfanoni, bunƙasa masana'antu, jawo masu zuba jari, da samar da damar ci gaban tattalin arziƙi da masana'antu a jihar.