Kanawa Post News

  • Home
  • Kanawa Post News

Kanawa Post News jaridar ta daya a arewa

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi ganawar ƙarshe da gawar Mawaƙi Kosan Waƙa
02/08/2026

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi ganawar ƙarshe da gawar Mawaƙi Kosan Waƙa

Hotuna: Gwamnatin jihar Kwara ta kammala tituna masu tsawon kilo mita 234.99Gwamna AbdulRahman Ya Ce Gina Hanyoyi Na Haɗ...
02/08/2026

Hotuna: Gwamnatin jihar Kwara ta kammala tituna masu tsawon kilo mita 234.99

Gwamna AbdulRahman Ya Ce Gina Hanyoyi Na Haɗa Jama'a Da Damar Ci Gaba

Gwamnatin Jihar Kwara ta ce tana ci gaba da aiwatar da manyan ayyukan gine-ginen hanyoyi da nufin inganta sufuri, rage cunkoson ababen hawa da kuma buɗe ƙarin damar tattalin arziki ga al'ummomin jihar.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ƙarƙashin shirin Rahman Legacy Series, gwamnatin ta bayyana cewa manyan ayyuka irin su gadar sama ta General Tunde Idiagbon Flyover, da Dr. Ibrahim Sulu-Gambari (Unity) Flyover, tare da sake gina manyan hanyoyi a sassa daban-daban na jihar, sun taimaka wajen sauƙaƙa zirga-zirga da haɗa al'ummomi da damammakin ci gaba.

Sanarwar ta ƙara da cewa an kammala gina hanyoyi masu tsawon kilomita 357.19, yayin da ake ci gaba da aikin wasu hanyoyi masu tsawon kilomita 234.99. Haka kuma, an aiwatar da fiye da ayyukan hanyoyi 160 na interlocking a faɗin jihar.

A cewar gwamnatin, waɗannan ayyukan sun sa ababen more rayuwa s**a zama muhimmin ginshiƙi na bunƙasa tattalin arziki da ci gaban al'umma a Jihar Kwara.

Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa manufar gwamnatin ba wai gina hanyoyi don sauƙaƙa zirga-zirga kaɗai ba ce, illa dai haɗa jama'a da damammakin rayuwa da ci gaba.

Kotu ta yanke wa wata budurwa hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan Yari saboda yanke al'aurar saurayinta a EkitiBabbar...
01/08/2026

Kotu ta yanke wa wata budurwa hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan Yari saboda yanke al'aurar saurayinta a Ekiti

Babbar kotun jihar Ekiti da ke zamanta a Ado-Ekiti ta yanke wa wata mata mai suna Joy Ikoja mai shekaru 35 hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan yari bayan samunta da laifin yanke gaban saurayinta, Ibrahim Usman.

An gurfanar da Ikoja ne kan tuhume-tuhume biyu da s**a hada da yunkurin kisa da kuma haddasa munanan raunuka, bayan wani rikici da ya faru a ranar 12 ga Afrilu, 2025.

Kotun ta ji cewa Ikoja ta k**a saurayinta tare da wata kawarta a daki, lamarin da ya haddasa rikici inda ake zarginta da murde masa al'aura, wanda ya janyo masa mummunan rauni har aka garzaya da shi asibiti domin ceto rayuwarsa.

A yayin shari'ar, masu gabatar da kara sun gabatar da shaidu hudu da hujjoji da s**a hada da rahoton likita da bayanan binciken 'yan sanda. Sai dai wacce ake tuhuma ta musanta aikata laifin tare da cewa ba ta jikkata saurayin nata ba.

A hukuncin da Mai Shari'a Oyinkansola Oluboyede ta yanke, kotun ta wanke Ikoja daga zargin yunkurin kisa saboda rashin isassun hujjojin da ke nuna niyyar kashe wanda abin ya shafa. Sai dai kotun ta same ta da laifin haddasa munanan raunuka, tare da yanke mata hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan yari.

Gwamna Bago Ya Yabawa Ɗangote Kan Bunƙasa Harkokin Masana'antu a Nijeriya da Afrika Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru B...
30/07/2026

Gwamna Bago Ya Yabawa Ɗangote Kan Bunƙasa Harkokin Masana'antu a Nijeriya da Afrika

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya yaba wa Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote kuma fitaccen attajirin Afrika, Alhaji Aliko Dangote, bisa jajircewarsa wajen bunƙasa ƙwarewa da bai wa al'umma damar ci gaba tun daga matakin ƙasa.

Gwamnan ya yi wannan yabo ne yayin wata ziyarar aiki da ya kai matatar mai da masana'antar sinadarai ta Dangote da ke Lekki a Jihar Legas.

A lokacin ziyarar, Gwamna Umaru Bago tare da Ƙaramin Ministan Masana'antu, Sanata John Owan Enoh, sun samu tarba daga Shugaban kuma Babban Daraktan Rukunin Kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote.

Gwamnan ya bayyana Aliko Dangote a matsayin jagora kuma abin koyi da ya samar wa 'yan Najeriya, musamman matasa, damar haɓaka basira da ƙwarewarsu.

Ya ce matatar mai ta Dangote ta zama wata muhimmiyar cibiyar koyon ilimi da ƙwarewa ga 'yan Afirka a fannin masana'antar man fetur da sinadarai. Ya kuma yaba wa Aliko Dangote kan wannan gagarumin aiki, wanda ya ce ya ɗaga martabar Najeriya da nahiyar Afirka a idon duniya.

A nasa jawabin, Alhaji Aliko Dangote ya gode wa Gwamna Umaru Bago bisa ziyarar da ya kai masa, sannan ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ƙara bai wa masu zuba jari na cikin gida cikakken goyon baya, yana mai cewa su ne za su taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasa.

Dangote ya ƙara da cewa samar da yanayi mai kyau ga masu zuba jari na cikin gida zai kuma ƙara jawo hankalin masu zuba jari daga ƙasashen waje.

Daga bisani, Aliko Dangote ya zagaya da gwamnan da tawagarsa domin duba manyan cibiyoyin masana'antu na zamani da ke cikin matatar mai.

Cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labaran gwamnan Ibrahim Bologi ya fitar, ta ce wannan ziyara ta nuna ƙudirin Gwamnatin Jihar Neja na ƙarfafa haɗin gwiwa da manyan kamfanoni, bunƙasa masana'antu, jawo masu zuba jari, da samar da damar ci gaban tattalin arziƙi da masana'antu a jihar.

Gwamnatin Kano ta ƙulla yarjejeniya da kamfani mai zaman kansa domin inganta tsarin sarrafa sharaGwamnatin Jihar Kano ta...
28/07/2026

Gwamnatin Kano ta ƙulla yarjejeniya da kamfani mai zaman kansa domin inganta tsarin sarrafa shara

Gwamnatin Jihar Kano ta hannun Ma'aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi ta ƙulla yarjejeniyar aiki da kamfanin Certis Nigeria Limited domin inganta tsarin sarrafa shara a faɗin jihar.

Kwamishinan ma'aikatar, Dakta Dahiru Hashim, ya bayyana cewa yarjejeniyar na da nufin sauya tsarin sarrafa shara daga aikin jin ƙai na gwamnati zuwa tsarin da zai kasance mai ɗorewa kuma mai amfani ta fuskar tattalin arziki.

Ya ce a ƙarƙashin haɗin gwiwar, kamfanin zai samar da ƙwarewar fasaha wajen zamanantar da tsarin sarrafa shara, da inganta gudanar da cibiyoyin tace gurɓataccen ruwa, tare da taimakawa wajen tsara babban tsarin magudanan ruwa na Jihar Kano.

Dakta Hashim ya ƙara da cewa gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf na ci gaba da jajircewa wajen ƙulla haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da tsaftataccen muhalli, inganta lafiyar al'umma da kuma samar da ci gaba mai ɗorewa a jihar.

ABUN BURGEWA: An Hango Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso Wanda Kotu ta Kora Wato Hon Abdullahi Ghali Basaf Ya kom...
28/07/2026

ABUN BURGEWA: An Hango Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso Wanda Kotu ta Kora Wato Hon Abdullahi Ghali Basaf Ya koma Bakin Sana'arsa ta Dinki,bayan Kotu ta yi Fatali dashi daga kan Madafun Iko.

Wane Fata zaku Masa?.

Daga Saifullahi Lawal Imam.

Hotuna: Yadda Sanatan Kano ta tsakiya, Rufa'i Sani Hanga ya gana da magoya bayansa domin jin ra'ayin su game da makomar ...
26/07/2026

Hotuna: Yadda Sanatan Kano ta tsakiya, Rufa'i Sani Hanga ya gana da magoya bayansa domin jin ra'ayin su game da makomar sa a jam'iyyar NDC.

Hukumar tace fina-finai  ta Kano ta hana gudanar da 'After Party' da 'Hot Challenge' a wuraren biki Hukumar tace fina-fi...
25/07/2026

Hukumar tace fina-finai ta Kano ta hana gudanar da 'After Party' da 'Hot Challenge' a wuraren biki

Hukumar tace fina-finai da Ɗab'i ta jihar Kano ta ƙaddamar da sabon mataki na hana gudanar da dukkan wasannin "After Party" da "Hot Challenge" a wuraren gudanar da taruka (Event Centers) a faɗin jihar, musamman a lokutan shagulgulan bikin aure.

Wannan mataki ya fito ne a cikin wata sanarwar manema labarai da aka fitar ranar Juma'a, 24 ga Yuli, 2026, wadda babban jami’in yaɗa labarai na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman , ya sa wa hannu a madadin Shugaban Hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha.

A cewar hukumar, matakin ya zama dole biyo bayan lura da yadda waɗannan ɗabi'u ke ƙara bazuwa a tsakanin al'umma, al'amarin da hukumar ta bayyana a matsayin "al'adun Yammacin Turawa" da ke barazana ga mutunci da kimar al'adun Hausawa da kuma koyarwar addinin Musulunci a Jihar Kano.

"Ɗaukar wannan mataki ya zama wajibi domin sauke nauyin da doka ta ɗora wa hukumar na tsaftace harkokin nishaɗi da kuma tabbatar da cewa ana gudanar da tarukan jama'a cikin tsarin al'adu da koyarwar addini," in ji Shugaban Hukumar, Abba El-Mustapha.

Hukumomin Tokyo sun bukaci maza su rika sanya gajeren wando zuwa aikiGwamnatin Birnin Tokyo a ƙasar Japan ta ƙarfafa ma'...
23/07/2026

Hukumomin Tokyo sun bukaci maza su rika sanya gajeren wando zuwa aiki

Gwamnatin Birnin Tokyo a ƙasar Japan ta ƙarfafa ma'aikata su rage sanya kwat a lokacin zafi, tare da amincewa maza su rika zuwa ofis cikin gajeren wando, rigar T-shirt da takalman wasanni a ƙarƙashin shirin "Tokyo Cool Biz."

Rahotanni sun ce Gwamnar Tokyo, Yuriko Koike, ta ƙaddamar da sabon tsarin ne a watan Afrilu sai dai wasu mata sun yi ƙorafin cewa an tilasta musu kallon gashin ƙafafun maza kuma hakan yana takura musu.

Address

Zoo Road

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kanawa Post News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Kanawa Post News:

Shortcuts

  • Want your organization to be the top-listed Government Service?

Share