28/08/2026
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya yi alkawarin kawo ƙarshen matsalar tsaro a Nijeriya cikin shekara guda idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Atiku ya bayyana hakan ne yayin wata hira da BBC Hausa, inda ya ce gwamnatinsa za ta ɗauki matakan da s**a dace domin kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro cikin shekara ɗaya da hawanta mulki.
Tun bayan fara gangamin siyasa gabanin zaɓen 2027, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ƙara jan hankalin jama’a da wasu manufofinsa. Daga cikin su akwai alkawarinsa na dawo da tallafin man fetur, wanda ya jawo martani daga gwamnatin tarayya da kuma wasu ‘yan Najeriya.