04/08/2026
Shugaba Tinubu Ya Amince Ƙarin Albashi Wa Sojoji
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu Ya amince da albashi wa jami'an sojin ƙasar nan tsakanin kashi 30 cikin 100 da kashi 80 cikin 100, yayin da kimanin jami'an soji 250,000 zasu amfana daga wannan ƙari.
Ƙarin albashin wanda zai fara aiki a ranar 1 ga watan Satumba na bana, inda sojoji masu manyan matsayi sama da Kanar zasu samu ƙarin kashi 30 cikin 100 na albashin su, wanda dai dai wannan karin ne masu matsayin Birgediya-Janar da Manjo-Janar, da ma Lafttenant-Janar zasu samu.
Su kuwa Sojoji masu matsayin ƙasa da Kanar zuwa Warant Ofisa zasu samu ƙarin kashi 50 cikin 100 na albashin su, yayin da Masu zaman kansu zuwa Staf Sajent zasu samu ƙarin kashi 80 cikin 100 na albashisu.
Wannan sabon ƙarin albashi a cewar sanarwar da Mai Magana da Yawun Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, Bayo Onanuga ya sanya wa hannu a yau Talata 4/8/2026, tace zai ɗaga yawan albashin sojan kasan na shekara daga Naira miliyan dubu 660 zuwa Naira miliyan dubu 924.
Shugaba Tinubu ya jinjina wa jajircewa da sadaukarwar da jami'an sojin Najeriya keyi wajen daƙile ayyukan ƴan fashin daji da Masu sace mutane da sauran yan taadda a wasu sassan kasar.