Kebbi State Hisbah

Kebbi State Hisbah official page of kebbi state hisbah Board, cabinet office Birnin Kebbi

22/06/2026

HUKUMAR HISBAH TA JIHAR KEBBI TA CHAFKE WASU BATA GARI DAKE KARBAN KUDDI GA MASU LAIFI DA SUNAN SU JAMIAN HISBAH NE AMMA.NA BUGI

Yau litinin wata bayani da yafito da Dan leken asirrin farin kaya dake aiki.da hukumar Hisbah ya rubutama office shin su cewar yanzu haka akwai mutun biyu dake hannun hukumar Hisbah wadanda sunka shahara wajen karban kuddi ga mutane masu aikatar badala.da sunan su Yan Hisbah ne inda s**a k**a wani.mutum da yacce sun karbi.kuddi har #150,000 hannun sa Dan leken asirrin yace wayanda ake tuma sun tabbatar da karban kuddin har sun mai.da masa abin sa rahoton yaci.gaba da cewa wadanda da ake tuma ba maaikatan Hisbah bane k**ar yadda rahoton ya bayyana dayan maaikacin Yan Banga ne dayan kuma maaikacin hukumar gyaran hali ne ta kasa inda shi Dan leken asirrin ya sanar da offishin su don sanin abin da ake ciki da kuma daukar matakin na gaba.

12/06/2026

WASU SAMARI SUN SHIRYA YIN AUREN DA BA MASA NIYAR IYAYENSU KO WALI DAGA KOWANE
BANGARE, SUN SHIGA HANNUN HISBAH

A jiya Alhamis, 11/06/2026, Hukumar Hisbah ta Jihar Kebbi ta samu nasarar dakile wani yunƙurin aure da wasu matasa s**a shirya gudanarwa ba tare da sani ko amincewar iyayensu ba.

Binciken farko ya nuna cewa matasan sun gayyaci abokai da ƙawaye domin halartar da kuma gudanar da wannan aure ba tare da bin ƙa'idodi da sharuddan da Shari'a da doka s**a tanada ba.

Hukumar Hisbah ta samu rahoton wannan al'amari ne daga wani mazaunin unguwar Nassarawa da ke Birnin Kebbi, inda jami'anta s**a gaggauta kai dauki tare da dakatar da shirin kafin a aiwatar da shi.

A halin yanzu, Hukumar na ci gaba da gudanar da cikakken bincike domin gano hakikanin yadda lamarin ya kasance da kuma ɗaukar matakan da s**a dace bisa tanadin doka.

Hukumar Hisbah tana jan hankalin matasa da su guji shiga duk wani al'amari da ya shafi aure ba tare da bin hanyoyin da Shari'a da doka s**a tanada ba, musamman samun yardar iyaye da waliyyai. Haka kuma tana kira ga iyaye da su ƙara sanya ido kan harkokin 'ya'yansu tare da ba su tarbiyya da shawarwari masu kyau domin kaucewa fadawa cikin irin waɗannan matsaloli.

03/02/2026

CIGIYA / KIRA GA JAMA’A
A yau 3/2/2026, Hukumar Hisbah ta samu rahoto game da wata budurwa da ta ɓace tun ranar Juma’a da ta gabata, mai suna Nusaiba Isah, mazauniyar bayan Ofishin C.I.D, Birnin Kebbi.
Hukumar Hisbah na kira ga duk wanda ya gani ko ya samu labarin inda take, da ya gaggauta sanar da Hukumar Hisbah kai tsaye, ko kuma ya kira lambobin da ke ƙasa:
📞 07037750371
📞 08153336523
Gudunmawar ku za ta taimaka matuƙa wajen gano ta da dawo da ita lafiya.
Allah Ya saka da alheri.

03/02/2026

AURE BA TARE DA SANIN UWAYEN MA'AURATAN BA
A ranar 2/2/2026, Hukumar Hisbah ta samu nasarar cafke wasu yara da s**a aikata auren ba bisa ka’ida ba, wato ba tare da sani ko amincewar iyayensu ba, a wani otel da ke Birnin Kebbi.
Binciken farko ya nuna cewa malamin da ya daura auren ya gudanar da daurin auren ne a inda:
abokin yaron ya tsaya a matsayin waliyin yarinyar,
yayin da yaron kuma ya karɓa wa kansa aure ba tare da sahihin waliyyi ba.
Haka kuma, an gano cewa yarinyar ’yar’uwar mahaifiyarsa ce, tare da hadin kai da abokinsa, wanda ake zargi suna da hannu kai tsaye a wannan daurin aure. Dukkan wadanda lamarin ya shafa an k**a su tare da gabatar da su gaban hukumomin da s**a dace domin ci gaba da bincike da kuma daukar hukuncin da ya dace, bisa tanadin shari’a da doka.
Hukumar Hisbah tana kira ga iyaye, malamai da al’umma baki ɗaya da su:
Guji daurin aure ba tare da ingantaccen waliyyi ba
Tabbatar da bin ka’idojin Shari’ar Musulunci da dokokin kasa
Kara kulawa da sa ido kan tarbiyya da mu’amalar ’ya’ya
Hukumar Hisbah za ta ci gaba da jajircewa wajen kare addini, tarbiyya da mutuncin al’umma.
Allah Ya shirya al’amuranmu.

Assalamu Alaikum Amadadin Hukumar Hisbah ta Argungu local government Muna Neman iyayan wannann yaro da aka tsinta wani m...
02/01/2026

Assalamu Alaikum Amadadin Hukumar Hisbah ta Argungu local government Muna Neman iyayan wannann yaro da aka tsinta wani massalaci Nan cikin gari Argungu, yaron yace sunan shi Yusuf, sunan baban shi baban Amera sunan mamarsa mamar Amera yace shi Dan garin sokoto ne Yanzu haka Yana office Hisbah na Argungu domin Neman karin bayani ku kira wannann numbars 07061308253 da fatar Allah ya sa a dace Amin

Address

Cabinet Office Birnin Kebbi
Birnin-Kebbi
860101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kebbi State Hisbah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share