Hon Adamu Muh'd Gargajiga For Reps 2023

Hon Adamu Muh'd Gargajiga For Reps 2023 Hon Muhammad Adamu GARGAJIGA For Reps Gombe/Kwami/Funakaye

HON ADAMU MUHAMMAD GARGAJIGA YA KADDAMAR DA KOMITIN YAKIN NEMAN ZABENSA. Ajiya ne Hon Adamu Muhammad Gargajiga, Dan Taka...
26/11/2022

HON ADAMU MUHAMMAD GARGAJIGA YA KADDAMAR DA KOMITIN YAKIN NEMAN ZABENSA.

Ajiya ne Hon Adamu Muhammad Gargajiga, Dan Takaran Majalisar Taraiya GKF ya kaddamar da komitin yakin neman zabensa, inda ya zakulo mutane masu hazaka a yankin na Gombe/Kwami/Funakaye.

Allah Yabamu Nasara.

Abdul Katika M
Gargajiga Media Aide.

HON ADAMU GARGAJIGA YA GANA DA TSOFIN DALIBANSA NA MAKARANTAWata kungiyar tsofin daliban *Hon Adamu Muhammad Gargajiga* ...
20/11/2022

HON ADAMU GARGAJIGA YA GANA DA TSOFIN DALIBANSA NA MAKARANTA

Wata kungiyar tsofin daliban *Hon Adamu Muhammad Gargajiga* sun kawo masa ziyarar nuna goyon baya tareda bada gudumawa wajen ganin malamin nasu yayi nasara.

Yayin jawabin shugaban kungiyar yace abunda malamin nasu yayi na alkhairi lokaci yayi da zasu saka masa, a jawabin nasa yake cewa da malamin nasu bai kyautata musu yabasu ilimi yanda yakamata ba da bazasu zo inda yake ba, ammana sakamakon abunda yamusu lokacin da yake karantar dasu yasa sun hakura da maban bantan jam'iyu da suke abaya zasu had'a gaba daya a karkashin jam'iyar NNPP domin ganin malamin nasu yayi nasara.

A nashi jawaban Hon Adamu Muhammad Gargajiga yayi farin ciki sosai tareda godiya, da nuna cewa da bai kyautata musu abaya ba da bazasu yi yunkurin zuwa inda yake ba harda zummar bashi gudumawa.

Da wannan muke kara kira ga dukkan al'ummar Gombe/Kwami/Funakaye da mu watsar da siyasar ra'ayi muzabi cancanta domin dawo da wakilci nagari a yankin na Gombe ta arewa a zauren majalisa.

Allah yabamu nasara.

Gargajiga Media Team

GOMBE/KWAMI/FUNAKAYE FEDERAL CONSTITUENCY. Kamar yanda kowa yasani halartaccen dan jam'iyar PDP ne ni, kuma zan zab'i PD...
14/11/2022

GOMBE/KWAMI/FUNAKAYE FEDERAL CONSTITUENCY.

Kamar yanda kowa yasani halartaccen dan jam'iyar PDP ne ni, kuma zan zab'i PDP daga sama har kasa, amma banda Hon Yaya Bauchi Tongo, Cancanta zamubi a wannan kujerar.

Ina gabatar muku da Adamu Gargajiga Mohammed domin kawo karshen zaman kashe wando da gyangyadi gamida d'umama kujera a zauren majalisa.

Hon Gargajiga tsohon malamin makaranta ne wanda yasan matsalar al'umma da yanda zai magance su, yakamata mu watsar da siyasar akida a wannan kujera mubi cancanta.

Allah yabamu nasara.

GARGAJIGA AWARENESS TEAM SUN KAI ZIYARA GARIN BAJOGA KARAMAR HUKUMAR FUNAKAYE. A kokarin da wannan tawaga keyi karkashin...
22/10/2022

GARGAJIGA AWARENESS TEAM SUN KAI ZIYARA GARIN BAJOGA KARAMAR HUKUMAR FUNAKAYE.

A kokarin da wannan tawaga keyi karkashin jagorancin Hon Abdullahi Dankamaru na shiga lungu da sako na mabazar Gombe ta Arewa domin neman alfarma da tuntuba akan Hon Gargajiga mun kai ziyara garin Bajoga dake karamar hukumar Funakaye.

A ziyarar mun samu zantawa da wasu daga cikin jagororin tafiyar na wannan yanki dama sauran al'umma domin neman goyon baya da azo ayi Hon Gargajiga domin ceto wannan yanki daga kishin ruwan rashin wakilci nagari.

Kuma Alhamdulillahi kwalliya tabiya kudin sabulu, mutanen Funakaye sun karbe mu hannu biyu tareda mana alkawura na bada gudumawarsu dari bisa dari akan wannan manufa ta Hon Gargajiga.

Daga karshe muna mika sakon godiya ga al'ummar wannan yanki bisa goyon baya da suke bamu ta yanda duk inda kashiga maganar Hon Gargajiga akeyi.

Da yardar Allah muna tare da nasara.

GARGAJIGA SOCIAL MEDIA TEAM

HON GARGAJIGA ZONAL EXCO SUN KAI ZIYARA GARIN KWAMI. A wani ziyara da Hon GARGAJIGA Zonal Exco keyi karkashin jagorancin...
19/10/2022

HON GARGAJIGA ZONAL EXCO SUN KAI ZIYARA GARIN KWAMI.

A wani ziyara da Hon GARGAJIGA Zonal Exco keyi karkashin jagorancin shugaban kungiyar Hon Abdullahi Dankamaru sun kai ziyara wani bangare a cikin karamar hukumar Kwami domin ganawa da wasu daga cikin jagororin yankin.

Yayin ziyarar sun ziyarci dan takarar majalisar jiha na wannan yanki a karkashin jam'iyar NNPP.

A jawabin jagoran tafiyar Hon Abdullahi Dankamaru Abdul yayi kira ga al'ummar wannan yankin gamida neman goyon bayansu da azo ahada karfi da karfe wajen marawa Hon GARGAJIGA baya domin sauya kurman wakilci da wannan yanki yake fama dashi a majalisar taraiya.

A nashi jawabin dan takarar majalisar yayi godiya da ziyarar a madadin al'ummar wannan yanki gamida jadda goyon bayansa wajen ganin nasarar Hon GARGAJIGA dama jam'iyar NNPP baki daya.

Daga karshe muna kara kira ga al'ummar mazabar Gombe ta Arewa da muzo mu hada kai mu marawa Hon GARGAJIGA baya domin wakilci nagari a majalisar taraiya.

GARGAJIGA SOCIAL MEDIA TEAM

ZAB'EN NAGARTACCEN MUTUM SHINE HANYAR SAMUN WAKILCI NAGARI. Nagartan Hon Gargajiga Yakai A Ce Ya Rike Ko Wani Irin Mukam...
15/10/2022

ZAB'EN NAGARTACCEN MUTUM SHINE HANYAR SAMUN WAKILCI NAGARI.

Nagartan Hon Gargajiga Yakai A Ce Ya Rike Ko Wani Irin Mukami A Fannin Shugabanci

Kyawawan halayensa tareda tsammanta masa yin wakilci nagari da ayyukan alkhairai da yake yiwa al'umma ba dare ba rana yasa muke fata yazama a zauren majalisar taraiya Karkashin Jam'iyar NNPP.

Bazamu taba yin dana sanin tallata mutumin kirki ga al'ummar yankin Gombe, Kwami, Fukaye ba.

Hakan yasa muke kira ga al'ummar Gombe ta Arewa akan zab'en Hon. Adamu Gargajiga Mohammed domin kawo karshen matsalar yankin na rashin samun wakilci nagari da ayyukan cigaba, sakamakon kuskuren da mukayi a baya na tura kurma wanda bai taba tashi yayi magana a zauren majalisa ba ballanta ya gabatar da kudurin al'ummar da yake wakilta.

Muna kira ga al'ummar wannan yanki da mu marawa wannan bawan Allah baya don ganin mun kaishi zauren majalisa don samun wakilci nagari da ayyukan raya al'umma.

As we open our eyes to see the light of today, may we riches favours of Allah. May our dreams, focus, mission, desire, e...
14/10/2022

As we open our eyes to see the light of today, may we riches favours of Allah. May our dreams, focus, mission, desire, expectations and many more will be fulfilled Insha Allah. May we and our family, continue to enjoy Allah's help in every challenge of life, and grant us unlimited Mercy and endless Favour Fid-Duniya Wal Akhira & make AlJannah Firdausi our final abode Ameen ya Allah.

Jummah Mubarak

ASSALAMU ALAIKUM MUTANEN GOMBE, KWAMI DA FUNAKAYE. Muna Gabatar Muku Da Hon Adamu Muhammad Gargajiga (Malam) A Matsayin ...
12/10/2022

ASSALAMU ALAIKUM MUTANEN GOMBE, KWAMI DA FUNAKAYE.

Muna Gabatar Muku Da Hon Adamu Muhammad Gargajiga (Malam) A Matsayin Dan Takarar Majalisar Tarayya Domin Samun Wakilci Nagari.

Hakika mazabarmu ta Gombe, Kwami, Funakaye idan muka zabi Gargajiga zamu samu wakilci nagari a zauren majalisa.

A shekaru kusan takwas kowa yasan irin yanda wakilcin wannan yanki a majalisar taraiya ya kasance, babu wani da zamuce gashi an cimma sakamakon tura kurma wakilci.

A wasu mazab'u dake jihar nan da s**a samu wakilci mai inganci a majalisar taraiya munga irin cigaba da al'ummar suke samu saboda jajirtattun wakilai da s**a samu wajen shiga duk inda ya dace don samo abubuwan cigaba, sab'anin namu yankin.

Wannan kurman wakilci da muka tura yasa mukayi yunkurin canjawa da nagartacce, idan muka zab'i Hon Gargajiga munada tabbacin samun wakilci nagari da dukkanin aiyukan cigaba ba tareda nuna banbanci ko kabilanci ba.

Hon Adamu Gargajiga tsohon malamin makaranta ne yasan matsalolin al'umma da yanda za'a magance su, musamman mata da matasa, gamida girmama mutane da al'ummar yankin bai daya.

Allah yabamu nasara.

2023 GOMBE / KWAMI / FUNAKAYE SAI GARGAJIGA INSHA ALLAH. Allah yatabbatar mana da nasara a zaben dake tafe 2023 domin sa...
24/09/2022

2023 GOMBE / KWAMI / FUNAKAYE SAI GARGAJIGA INSHA ALLAH.

Allah yatabbatar mana da nasara a zaben dake tafe 2023 domin samun wakilci na gari a majalisan wakilen Nigeria.

GOMBE/KWAMI/FUNAKAYE FEDERAL CONSTITUENCY.   Don kawo karshen zaman kashe wando, gyangyad’i da d’umama kujera a zauren m...
07/09/2022

GOMBE/KWAMI/FUNAKAYE FEDERAL CONSTITUENCY.

Don kawo karshen zaman kashe wando, gyangyad’i da d’umama kujera a zauren majalisar tarayya gami da zazzare idanu ba tare da an fahimci meye yake gudana ba, mu zabi Hon. Adamu Muhammad Gargajiga don yin wakilci nagari a mazabar Gomne/Kwami/Funakaye.
ALLAH YA sa mu dace kuma YA ba mu nasara,

GOMBE, KWAMI, FUNAKAYE LOKACI YAYI HON GARGAJIGA FOR REPS.   Mu al’ummar Gombe, Kwami da Funakaye zai yi wuya mu sake sa...
06/09/2022

GOMBE, KWAMI, FUNAKAYE LOKACI YAYI HON GARGAJIGA FOR REPS.

Mu al’ummar Gombe, Kwami da Funakaye zai yi wuya mu sake sakewa a yi mana sakiya karo na biyu, dole mu dawo da wikilin da bai san meye ya kai shi majalisa ba b***e yayi mana wakilci na gari.

Al'ummar Gombe Kwami, Funakaye muna gabatar muku da Hon Adamu Muhammad Gargajiga domin wakilci nagari.

Address

Gombe/Kwami/Funakaye
Gombe
08145444585

Telephone

+2349012898988

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hon Adamu Muh'd Gargajiga For Reps 2023 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to Hon Adamu Muh'd Gargajiga For Reps 2023:

Share