21/08/2022
GARABASA GUDA BIYAR GA DUK
WANI MU'MINI
1. Ko kasan cewa yayin idar da kiran Sallah karka haramtawa kanka Addu'ah, domin Addu'ah a wannan lokaci ba'a juyata.
2. Ko kasan ina ake sanya zunuban
ka yayin da kake sallah?
Manzon Allah (saw) ya ce:- "Duk
lokacin da bawa ya ke Sallah ana
sanya dukkan zunuban sa a wuyan
sa da kafadun sa, duk lokacin da ya yi
ruku'u ko sujada zunuban sa za su dinga fadowa kamar yadda ganye yake fadowa daga bishiya ."
Yakai wanda kake gaggawa ya yin ruku'u ko sujada, ka tsawaita sujada da ruku'u domin zunuban ka su ragu kada ka bari wannan garabasa ta wuce ka.
3. Ko kasan wata salihar mace ta
rasu, duk lokacin da 'yan uwanta s**a ziyarci kabarin ta sai suji kamshi yana tashi, sai s**a tambayi mijinta sai ya ce ta kasance tana karanta Suratul
Mulk kowane dare kafin tayi bacci.
4. Ko kasan karanta Ayatul
Kursiyyu bayan kowace sallah zaka
wayi gari tsakanin ka da Aljannah
mutuwace kadai?
5. Ko kasan idan ka idar da sallah kar kayi gaggawar tashi, domin mala'iku suna roka maka gafara.
👆Ya Allah ka sanya wannan tunatarwa ta zama SADAKATUL JARIYA a gareni da Iyayena da duk wanda ya taimaka wajan yadawa,
Amin