Anas kwami

Anas kwami Islamic Preaching

31/05/2021

Sako daga fadar manzo (saw) (4).

Abdullahi Dan Abbas yace manzon Allah saw ya wuce kaburbura guda biyu sai yace ma,abota wadannan kaburbura ana musu azaba, ba ana musu azaba ne akan babban zunubin da kaurace masa yakeda wahala ba,

Daya daga cikin su baya suturtuwa daga fitsari, dayan kuma ya kasance yana watsa annamimanci ......

Abubuwan da zamu koya a wannan hadisin:

** Tabbatar da cewa lallai akwai azabar kabari

** Rashin tsarkaka daga fitsari yana sabbaba azaban kabari

** Haramcin annamimanci Wanda shine daukan magana wani ka kaiwa wani domin haddasa gaba da husuma a tsakaninsu

** Annamimanci yana daga cikin ayyukan sabon da suke haddasa azabar kabari

Allah ya bamu ikon kiyayewa.

28/05/2021

Sako daga fadar manzo(1).

Manzon Allah صلى الله عليه و سلم yace " ALLAH BAYA KARBAN SALLAH DAYANKU IDAN YAYI HADASI HAR SAI YAYI ALWALA"

Hadasi shine abunda yake fitowa daga mafita guda biyu kamar fitsari ko bayan gari ko wanin wadannan.

Abubuwan da zamu koya daga wannan hadisin sune

** Allah baya karban sallah mai hadasi har sai yayi alwala.

** yin hadasin yana bata alwala

** ingancin alwala yana daga sharadin karban sallah.

Allah ya bamu ikon kiyayewa.

Haunas Kwami
11/12/2019.

03/12/2020

Bashi a musulunci (1)

Bada Bashi mai kyau wani kusanci ne Wanda musulmi yake kusantar Allah dashi saboda abunda yake cikinsa na tausayawa al,umma da kuma rangwanta musu da yaye musu halin kunci da bakin Cikin da suke tare dashi

Hakika duk Wanda Allah ya azurtashi da dukiya abun sone agareshi ya zamo mai taimakawa na kasa dashi a dukkan lokacin da s**a bukaci taimakonsa in ma kyauta ko sadaka ko kuma basu bashin da zasu dawo masa dashi.

Kamar yadda ya halatta ga mutumin dayake Cikin matsi ko kuncin rayuwa daya karbi bashi domin ya biya bukatarsa ya samu saukin al,amarin dayake ciki.

Saidai haramun ne karban bashi sannan a sanya abunda aka karba a Sabon Allah kamar yadda yake sanenne a wurin mafi yawan musulmai cewa akwai tambaya akan dukiya TA INA KA SAMU SANNAN TA INA KA KASHE sabida haka wajibine ga mai cin bashi ya zama ya sanya abunda aka bashi wajen biyayya ga Allah banda Saba masa, sannan ya dawo masa da kwatankwacin abunda ya karba

Saidai dukkan bashin da zai jawo wani amfani kamar bashin dake dauke da riba (interest ) wannan kam haramun ne a Shari,ance kamar yadda ayoyi da hadisai s**ayi nuni akan hakan.

Allah ya bamu ikon kiyayewa

Sai mun hadu a fitowa ta gaba.

✍️✍️✍️
Anas Jibir.

03/09/2020

Abokin hira.

Prof mansur sokoto.

2.Gamon Katar:

Varawo ya Zama Sarki

Wani varawo ne aka yi mashiririci mai suna Katar. Watarana ya shiga Masallaci don ya yi sata a tsakiyar dare. Da shigar sa sai ya ji motsin mutane kusa da Masallacin. Da ya ji sun matso kusa sai ya kabbarta Sallah.

Ana haka sai ya ji an bude Masallaci an shigo. Sai ya yanke shawarar tsawaita Sallah saboda jin tsoro. Su kuma kawai sai s**a share wuri s**a zauna suna jiran sa. A tsorace ya sallama ya waiga don ya ga ko su wane ne. Ko da ya juya sai ya ga Sarki da tawagarsa. Kafin ya ce komai sai Sarki ya miqa masa hannu s**a gaisa, bai san abinda ke faruwa ba. Aka je da shi fada aka kyautata masa har gari ya waye sannan aka yi yekuwa. Jama’a s**a taru sannan sai Sarki ya yi jawabi.

Ya ce, tun da dadewa ina son in aurar da babbar ‘yata. Kuma na rasa wanda zan aura ma ita domin ina neman na kirki mai jin tsoron Allah. Amma Liman ya ba ni shawara kuma na yi aiki da ita. Na samu wannan saurayi a tsakiyar dare shi kadai cikin Masallaci yana sallah a lokacin da duk ire-irensa suna gida suna bacci.

Don haka na aura masa da ‘yata kuma na yanka masa wani babban gari daga cikin masarautata.

A nan ne fa gogan naka ya sunkuyar da kansa yana kuka, yana fadi a zuciyarsa, wannan fa sallar qarya ce na yi Allah ya ba ni wannan alheri. To, ina ga na yi sallar gaskiya! Ya Allah daga yau na daina duk wani aikin assha, kuma zan riqa sallar dare har iya tsawon rayuwata.

To, kun ji labarin “Katar” da ake cewa: Allah ya yi muna gamon Katar.

Darussa:

-A rana daya Allah kan yi bature.
Duk halin da ka ga mutum a cikin sa kada ka yanke masa qauna. Idan yana da rabo watarana Allah zai shirya shi.

-Kada ka rudu kawai da zahirin mutum. Da yawa akwai rina a qarqashin kaba ba ka sani ba

11/06/2020

alimullah Ahmad Hinna
MENE NE YAN MADAKHILA (MURJI'A) SUKE TANTAMA DA
BANKAURA AKAI GAME DA KAFA QUNGIYA?
Ts**akken shirmen furucin su irin ta Manhajin Madakhila
(Murji'a) shine, yawan maimaita cewa mu Yan Qungiya ne
(Hizbiyoun). Rashin sanin Nassoshi da rashin dogon nazari kan
maganganun magabata ke sanya mutum kaji yana wannan irin
furuci ta Jahilci. Wa yace maka don mutum yana Qungiya ya fita
daga Da'irar Sunnah? Matukar Dan qungiya yana kan tafarkin
Sunnah da kiyaye dokokin Allah, ko shakka babu, babu abunda ya
fitar dashi daga Sunnah. Mafi illar dake sanya Qungiya ta zama
abun zargi shine wuce gona da iri wajen nuna Ta'assubanci ko
Guluwwiy kan ita Qungiyyar da zimmar duk wanda bai shiga
Qungiyar ka ba koda yana bin Qur'ani da sunnah sai ka dinga
ganin sa ba akan daidai yake ba, to daga nan kowace irin
Qungiya kake, ko shakka babu ya zama abun zargi da tuhuma
dalilin ta'assubancin da ka nuna, aikata hakan Qungiyanci ne.
Idan kuma nazarin ka bai kai nan ba kai mai yawan ambaton
cewa mu Yan Qugiya ne (Hizbiyyoun) saboda wata son zuciya
irin taka. Ga abunda Allah madaukain sarki yake cewa:
ﻭَﻟْﺘَﻜُﻦ ﻣِّﻨﻜُﻢْ ﺃُﻣَّﺔٌ ﻳَﺪْﻋُﻮﻥَ ﺇِﻟَﻰ ﺍﻟْﺨَﻴْﺮِ ﻭَﻳَﺄْﻣُﺮُﻭﻥَ ﺑِﺎﻟْﻤَﻌْﺮُﻭﻑِ ﻭَﻳَﻨْﻬَﻮْﻥَ ﻋَﻦِ ﺍﻟْﻤُﻨﻜَﺮِ ﻭَﺃُﻭْﻟَﺌِﻚَ ﻫُﻢُ
ﺍﻟْﻤُﻔْﻠِﺤُﻮﻥَ
ﺁﻝ ﻋﻤﺮﺍﻥ 104
Fassara:
"A cikin ku a samu wata al'umma wanda zasu ke ƙira ga alkairi
kuma suke umarni da kyakkyawa suna hani daga mummuna,
wadancan sune maus rabauta"
YANDA MALAMAN TAFISIRI S**A FASSARA:
Bari muga manyan Malaman tafsiri me s**a ce game da wannar
Ayah. Ga abunda Ibnu Kathir yake cewa:
ﺍﺑﻦ ﻛﺜﻴﺮ : ﻭَﻟْﺘَﻜُﻦ ﻣِّﻨﻜُﻢْ ﺃُﻣَّﺔٌ ﻳَﺪْﻋُﻮﻥَ ﺇِﻟَﻰ ﺍﻟْﺨَﻴْﺮِ ﻭَﻳَﺄْﻣُﺮُﻭﻥَ ﺑِﺎﻟْﻤَﻌْﺮُﻭﻑِ ﻭَﻳَﻨْﻬَﻮْﻥَ ﻋَﻦِ ﺍﻟْﻤُﻨﻜَﺮِ ۚ
ﻭَﺃُﻭﻟَٰﺌِﻚَ ﻫُﻢُ ﺍﻟْﻤُﻔْﻠِﺤُﻮﻥَ
ﻭﺍﻟﻤﻘﺼﻮﺩ ﻣﻦ ﻫﺬﻩ ﺍﻵﻳﺔ ﺃﻥ ﺗﻜﻮﻥ ﻓﺮﻗﺔ ﻣﻦ ﺍﻷﻣﺔ ﻣﺘﺼﺪﻳﺔ ﻟﻬﺬﺍ ﺍﻟﺸﺄﻥ ، ﻭﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﺫﻟﻚ
ﻭﺍﺟﺒﺎ ﻋﻠﻰ ﻛﻞ ﻓﺮﺩ ﻣﻦ ﺍﻷﻣﺔ ﺑﺤﺴﺒﻪ ، ﻛﻤﺎ ﺛﺒﺖ ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﻣﺴﻠﻢ ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓ ﻗﺎﻝ
: ﻗﺎﻝ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ : " ﻣﻦ ﺭﺃﻯ ﻣﻨﻜﻢ ﻣﻨﻜﺮﺍ ﻓﻠﻴﻐﻴﺮﻩ ﺑﻴﺪﻩ ، ﻓﺈﻥ ﻟﻢ
ﻳﺴﺘﻄﻊ ﻓﺒﻠﺴﺎﻧﻪ ، ﻓﺈﻥ ﻟﻢ ﻳﺴﺘﻄﻊ ﻓﺒﻘﻠﺒﻪ ، ﻭﺫﻟﻚ ﺃﺿﻌﻒ ﺍﻹﻳﻤﺎﻥ . " ﻭﻓﻲ ﺭﻭﺍﻳﺔ : "
ﻭﻟﻴﺲ ﻭﺭﺍﺀ ﺫﻟﻚ ﻣﻦ ﺍﻹﻳﻤﺎﻥ ﺣﺒﺔ ﺧﺮﺩﻝ " .
Fassara:
"Abunda ake nufi daga wannar Ayar shine, ta kasamce
"QUNGIYA" daga al'ummah tsayayyu domin wannan sha'ani, idan
hakan ya ksance wajibi ne akan kowa mutum da cikin al'ummah
gwargwadon sa, kamar yanda ya tabbata a cikin Sahihu Muslim.
Daga Abu Huraira (Allah ya qara masa yarda), yace: Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare shi yace: "Duk
wanda yaga abun qi, toh ya chanja shi da hannun sa, idan bazai
iya ba, yayi da harshen sa, idan bazai iya ba, yayi zuciyar sa.
Wannan shine mafi raunin Imani" A cikin wata riwaya ta daban:
Babu abunda ke bayan haka daga Imani daidai da qwayar zarra"
Ga kuma abunda Imam Addabariy yake cewa cikin tafsirin sa:
ﺍﻟﻄﺒﺮﻯ : ﺍﻟﻘﻮﻝ ﻓﻲ ﺗﺄﻭﻳﻞ ﻗﻮﻟﻪ : ﻭَﻟْﺘَﻜُﻦْ ﻣِﻨْﻜُﻢْ ﺃُﻣَّﺔٌ ﻳَﺪْﻋُﻮﻥَ ﺇِﻟَﻰ ﺍﻟْﺨَﻴْﺮِ ﻭَﻳَﺄْﻣُﺮُﻭﻥَ
ﺑِﺎﻟْﻤَﻌْﺮُﻭﻑِ ﻭَﻳَﻨْﻬَﻮْﻥَ ﻋَﻦِ ﺍﻟْﻤُﻨْﻜَﺮِ ﻭَﺃُﻭﻟَﺌِﻚَ ﻫُﻢُ ﺍﻟْﻤُﻔْﻠِﺤُﻮﻥَ ‏( 104 )
ﻗﺎﻝ ﺃﺑﻮ ﺟﻌﻔﺮ : ﻳﻌﻨﻲ ﺑﺬﻟﻚ ﺟﻞ ﺛﻨﺎﺅﻩ: " ﻭﻟﺘﻜﻦ ﻣﻨﻜﻢ " ﺃﻳﻬﺎ ﺍﻟﻤﺆﻣﻨﻮﻥ "= ﺃﻣﺔ " ، ﻳﻘﻮﻝ:
ﺟﻤﺎﻋﺔ ‏( 74‏) "= ﻳﺪﻋﻮﻥ " ﺍﻟﻨﺎﺱ"= ﺇﻟﻰ ﺍﻟﺨﻴﺮ " ، ﻳﻌﻨﻲ ﺇﻟﻰ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﻭﺷﺮﺍﺋﻌﻪ ﺍﻟﺘﻲ
ﺷﺮﻋﻬﺎ ﺍﻟﻠﻪ ﻟﻌﺒﺎﺩﻩ ‏( 75‏) "= ﻭﻳﺄﻣﺮﻭﻥ ﺑﺎﻟﻤﻌﺮﻭﻑ " ، ﻳﻘﻮﻝ: ﻳﺄﻣﺮﻭﻥ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺑﺎﺗﺒﺎﻉ ﻣﺤﻤﺪ
ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻭﺩﻳﻨﻪ ﺍﻟﺬﻱ ﺟﺎﺀ ﺑﻪ ﻣﻦ ﻋﻨﺪ ﺍﻟﻠﻪ ‏( 76 ‏) " ﻭﻳﻨﻬﻮﻥ ﻋﻦ ﺍﻟﻤﻨﻜﺮ " ،:
ﻳﻌﻨﻲ ﻭﻳﻨﻬﻮﻥ ﻋﻦ ﺍﻟﻜﻔﺮ ﺑﺎﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﺘﻜﺬﻳﺐ ﺑﻤﺤﻤﺪ ﻭﺑﻤﺎ ﺟﺎﺀ ﺑﻪ ﻣﻦ ﻋﻨﺪ ﺍﻟﻠﻪ، ﺑﺠﻬﺎﺩﻫﻢ
ﺑﺎﻷﻳﺪﻱ ﻭﺍﻟﺠﻮﺍﺭﺡ، ﺣﺘﻰ ﻳﻨﻘﺎﺩﻭﺍ ﻟﻜﻢ ﺑﺎﻟﻄﺎﻋﺔ .
(74) ﺍﻧﻈﺮ ﺗﻔﺴﻴﺮ" ﺃﻣﺔ" ﻓﻴﻤﺎ ﺳﻠﻒ :1 221 / :3 74 ، 100 ، 128 ، 141 ، 275 -
277.
(75) ﺍﻧﻈﺮ ﺗﻔﺴﻴﺮ" ﺍﻟﺨﻴﺮ " ﻓﻴﻤﺎ ﺳﻠﻒ :2 505 .
(76) ﺍﻧﻈﺮ ﺗﻔﺴﻴﺮ "ﺍﻟﻤﻌﺮﻭﻑ " ﻓﻴﻤﺎ ﺳﻠﻒ :3 293 / 4 : 547 ، 548 / : 5 44 ، 76 ،
93 ، 137 ، 520 .
Fassara:
"Abu Ja'afar yace: Abunda Allah yake nufi da hakan shine: Ya
kasamce wata al'ummah daga cikin ku" Ku muminai wata
al'ummah" yana cewa: Jama'a (Qungiya), suna kiran mutane
zuwa ga alkhairi" yana nufin zuwa ga musulunci da Shari'o'in sa
wadanda Allah ya shar'anta ga bayin sa. "Su dinga umurni da
kyawawa ayyuka" yana nufin su dinga umurtan mutane da bin
Muhammad tsira da amincin Allah sh tabbata gare shi, da
Addinin sa wanda yazo dashi daga Allah. "Su dinga hani da abun
qi" ma'ana: Su dinga hani game da kafurci da Allah da qaryata
Muhammad da abunda yazi dashi daga Allah. Da jihadin su da
hannu da ga66ai har sun zama masu biyayyah"
MATSAYIN YIN QUNGIYA DAGA BAKIN MANYAN MALAMAN
SUNNAH. WA YACE MAKA YIN QUNGIYA LAIFI NE?
Bayan wancar Ayah da bayanin ta ya gabata daga manyan
Malaman tafsiri. Ga kuma abunda Manyan Malamai wanda s**a
gabace mu da wadanda muka yi zamani tare dasu suke cewa.
Shaykhul Islma yana cewa:
ﻳﻘﻮﻝ ﺷﻴﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ: " ﻭﺃﻣﺎ ‏[ ﺭﺃﺱ ﺍﻟﺤﺰﺏ ‏] ﻓﺈﻧﻪ ﺭﺃﺱ ﺍﻟﻄﺎﺋﻔﺔ
ﺍﻟﺘﻲ ﺗﺘﺤﺰﺏ، ﺃﻯ ﺗﺼﻴﺮ ﺣﺰﺑًﺎ، ﻓﺈﻥ ﻛﺎﻧﻮﺍ ﻣﺠﺘﻤﻌﻴﻦ ﻋﻠﻰ ﻣﺎ ﺃﻣﺮ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻪ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ ﻣﻦ
ﻏﻴﺮ ﺯﻳﺎﺩﺓ ﻭﻻ ﻧﻘﺼﺎﻥ ﻓﻬﻢ ﻣﺆﻣﻨﻮﻥ، ﻟﻬﻢ ﻣﺎ ﻟﻬﻢ ﻭﻋﻠﻴﻬﻢ ﻣﺎ ﻋﻠﻴﻬﻢ. ﻭﺇﻥ ﻛﺎﻧﻮﺍ ﻗﺪ ﺯﺍﺩﻭﺍ
ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻭﻧﻘﺼﻮﺍ ﻣﺜﻞ ﺍﻟﺘﻌﺼﺐ ﻟﻤﻦ ﺩﺧﻞ ﻓﻲ ﺣﺰﺑﻬﻢ ﺑﺎﻟﺤﻖ ﻭﺍﻟﺒﺎﻃﻞ، ﻭﺍﻹﻋﺮﺍﺽ ﻋﻤﻦ
ﻟﻢ ﻳﺪﺧﻞ ﻓﻲ ﺣﺰﺑﻬﻢ، ﺳﻮﺍﺀ ﻛﺎﻥ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺤﻖ ﻭﺍﻟﺒﺎﻃﻞ، ﻓﻬﺬﺍ ﻣﻦ ﺍﻟﺘﻔﺮﻕ ﺍﻟﺬﻯ ﺫﻣﻪ ﺍﻟﻠﻪ
ﺗﻌﺎﻟﻰ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ، ﻓﺈﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ ﺃﻣﺮﺍ ﺑﺎﻟﺠﻤﺎﻋﺔ ﻭﺍﻻﺋﺘﻼﻑ، ﻭﻧﻬﻴﺎ ﻋﻦ ﺍﻟﺘﻔﺮﻗﺔ
ﻭﺍﻻﺧﺘﻼﻑ، ﻭﺃﻣﺮﺍ ﺑﺎﻟﺘﻌﺎﻭﻥ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺒﺮ ﻭﺍﻟﺘﻘﻮﻯ، ﻭﻧﻬﻴﺎ ﻋﻦ ﺍﻟﺘﻌﺎﻭﻥ ﻋﻠﻰ ﺍﻹﺛﻢ
ﻭﺍﻟﻌﺪﻭﺍﻥ "
( ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ، ﺍﻟﻤﺠﻠﺪ 11 ﺻﻔﺤﺔ 92 ).
Fassara:
"Dangane da Jagorancin Qungiya, jagorancin al'ummah wacce
take gungiyantuwa, ma'ana ta zama wata Qungiya. Idan sun
kasance sun hadu ne kan abunda Allah da Manzon sa s**a yi
umurni dashi ba tare da yin qari ko ragi ba, su muminai ne.
Abunda ke nasu nasu ne, abunda ke kan su yana kansu. Idan ko
sun kasance sunyi qari cikin haka, kuma s**a yi ragi, misalin
Ta'assubanci ga wanda ya shiga Qungiyar su da abunda yake
gaskiya ko na 6ata, da juya baya ga wanda bai shiga Qungiyar su
ba, koda ace mai shi ya kasance akan gaskiya da 6ata. To
wannan shine irin Qumgiyacin da Allah madaukakin sarki ya
kushe shi da Manzon sa. Domin Allah da Manzon sa sunyi
umurni ne da Jama'a da hadin kai, da kuma hani game da
rarrabuwa da sa6ani. Kuma yayi umurni da taimakekeniya akam
nagarta da jin tsoron Allah, da hani kan taimakekeniya kan
zunubi da qiyayyah"
Bayan haka, ga maganar Sheikh Nasiriddeen Albaniy (Allah ya
masa rahama) dake qarfafuwa kan haka:
ﻗﺎﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﻣﺤﻤﺪ ﻧﺎﺻﺮ ﺍﻟﺪﻳﻦ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ : ‏« ﺃﻱُّ ﺟﻤﻌﻴﺔ ﺗﻘﺎﻡ ﻋﻠﻰ ﺃﺳﺎﺱٍ ﻣﻦ
ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺍﻟﺼﺤﻴﺢ، ﺍﻟﻤﺴﺘﻨﺒﻄﺔِ ﺃﺣﻜﺎﻣُﻬﺎ ﻣﻦ ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﻠﻪ، ﻭﻣﻦ ﺳﻨﺔ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ، ﻭﻣﻤﺎ ﻛﺎﻥ
ﻋﻠﻴﻪ ﺳﻠﻔﻨﺎ ﺍﻟﺼﺎﻟﺢ، ﻓﺄﻱُّ ﺟﻤﻌﻴﺔٍ ﺗﻘﻮﻡ ﻋﻠﻰ ﻫﺬﺍ ﺍﻷﺳﺎﺱ؛ ﻓﻼ ﻣﺠﺎﻝ ﻹﻧﻜﺎﺭﻫﺎ ﻭﺍﺗﻬﺎﻣﻬﺎ
ﺑﺎﻟﺤﺰﺑﻴﺔ؛ ﻷﻥ ﺫﻟﻚ ﻛﻠَّﻪ ﻳﺪﺧﻞ ﻓﻲ ﻋﻤﻮﻡ ﻗﻮﻟﻪ ﺗﻌﺎﻟﻰ : ‏( ﻭﺗﻌﺎﻭﻧﻮﺍ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺒﺮ ﻭﺍﻟﺘﻘﻮﻯ‏)
‏[ ﺍﻟﻤﺎﺋﺪﺓ 2:‏] ، ﻭﺍﻟﺘﻌﺎﻭﻥُ ﺃﻣﺮٌ ﻣﻘﺼﻮﺩ ﺷﺮﻋﺎً، ﻭﻗﺪ ﺗﺨﺘﻠﻒ ﻭﺳﺎﺋﻠﻪ ﻣﻦ ﺯﻣﻦ ﺇﻟﻰ ﺯﻣﻦ، ﻭﻣﻦ
ﻣﻜﺎﻥ ﺇﻟﻰ ﻣﻜﺎﻥ، ﻭﻣﻦ ﺑﻠﺪﺓ ﺇﻟﻰ ﺃﺧﺮﻯ، ﻭﻟﺬﻟﻚ ﻓﺎﺗﻬﺎﻡُ ﺟﻤﻌﻴﺔٍ ﺗﻘﻮﻡ ﻋﻠﻰ ﻫﺬﺍ ﺍﻷﺳﺎﺱِ
ﺑﺎﻟﺤﺰﺑﻴﺔِ ﺃﻭ ﺑﺎﻟﺒﺪﻋﻴﺔِ، ﻓﻬﺬﺍ ﻻ ﻣﺠﺎﻝ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﻘﻮﻝ ﺑﻪ، ﻷﻧﻪ ﻳﺨﺎﻟﻒ ﻣﺎ ﻫﻮ ﻣﻘﺮﺭ ﻋﻨﺪ
ﺍﻟﻌﻠﻤﺎﺀ ﻣﻦ ﺍﻟﺘﻔﺮﻳﻖ ﺑﻴﻦ ﺍﻟﺒﺪﻋﺔ ﺍﻟﻤﻮﺻﻮﻓﺔ – ﺑﻌﺎﻣﺔ – ﺑﺎﻟﻀﻼﻟﺔ، ﻭﺑﻴﻦ ﺍﻟﺴُّﻨﺔِ ﺍﻟﺤﺴﻨﺔ
(1) ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ، ﺳﻠﺴﻠﺔ ﺍﻟﻬﺪﻯ ﻭﺍﻟﻨﻮﺭ، ﺷﺮﻳﻂ ﺭﻗﻢ ‏( 590 ).
Fassara:
Kowace irin Jam'iyyah (Qungiya) da take tsaye akan ginshiqin na
Musulunci ingantacce, wacce aka ciro (Istimbadi), hukunce
hukucen ta daga littafin Allah (Qur'ani) da Sunnar Manzon Allah,
da abunda magabatan mu na qwarai s**a kasance akai. Duk
Jam'iyyar take tsaye kan wannan Ginshiqi, babu wani zancen a
dinga Inkarin ta da tuhumar ta da Qungiyanci, domin dukkan
hakan yana shiga cikin fadin Allah madaukakin Sarki: (Kuyi
taimakekeniya kan nagarta da jin tsoron Allah). Shiko
taimakekeniya al'amari ne da manufa a Shari'ance. Haqiqa
hakan yana sa6awa isarwar sa daga zamani zuwa zamani, dava
waje zuwa waje, daga gari zuwa ga wani garin. Saboda haka,
tuhumar irin wannan Jam'iyyah (Qungiya) da take tsaye kan
wannan ginshiqi da Qungiyanci ko da Bidi'anci, wannan sam bai
dace da furucin haka ba dashi. Domin ya sa6a da abunda yake
tabbatacce wajen manyan Malamai daga rarrabewa tsakanin
Bidi'a da abunda ake siffantawa, da kuma gamayyar da cewa
6ata ce da tsakanin Sunnah wacce mai kyau.
SHIN AKWAI ALKHAIRI CIKIN ASSASA QUNGIYA?. ME
MALAMAN SUNNAH S**A CE KAN HAKA?!
A cikin tsarin tafiyar da addini musulumci wajen taimakekeniya
tsakanin al'ummah kan abunda yake na nagarta da tsoron Allah
domin cigaban addinin musulumci bisa karantarwan Sunnah,
shine haduwar da babu zargi cikin ta matuqar hadafin su da
manufofin su shine daukaka kalmar Allah da Sunnah ta Manzon
Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata gare shi). Wanda hakan
shike halattuwa wajen assasa qungiya domin gudanar da ire iren
wadannan ayyuka na alkhairi. Kamar yanda muka sani, kowace
irin Qungiya tana zama abun zargi ne daga lokaci da aka sanya
Ta'aasubanci da Guluwwiy ko Taqalidanci cikin ta. Haka kuma,
Qungiya takan zama alkhairi da kuma albarka idan ya kasance
manufarta shine kawo cigaban addini da tabbatar da Sunnar
Manzon Allah. Ya za'ayi mu gane haka? Sannan daga bakin wa
ya kamata mu san abunda dake tattare da haka? Ba tareda
munyi nisa ba. Ga abunda Sheikh Abdul'Azeez Bin Baza (Allah ya
masa rahama) yake cewa:
ﻗﺎﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﺑﻦ ﺑﺎﺯ ـ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺍﻟﺠﻤﻌﻴﺎﺕ ﺇﺫﺍ ﻛﺜﺮﺕ ﻓﻲ ﺃﻱ ﺑﻠﺪ ﺇﺳﻼﻣﻲ ﻣﻦ ﺃﺟﻞ
ﺍﻟﺨﻴﺮ ﻭﺍﻟﻤﺴﺎﻋﺪﺍﺕ ﻭﺍﻟﺘﻌﺎﻭﻥ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺒﺮ ﻭﺍﻟﺘﻘﻮﻯ ﺑﻴﻦ ﺍﻟﻤﺴﻠﻤﻴﻦ، ﺩﻭﻥ ﺃﻥ ﺗﺨﺘﻠﻒ ﺃﻫﻮﺍﺀ
ﺃﺻﺤﺎﺑﻬﺎ ﻓﻬﻲ ﺧﻴﺮ ﻭﺑﺮﻛﺔ ﻭﻓﻮﺍﺋﺪﻫﺎ ﻋﻈﻴﻤﺔ، ﺃﻣﺎ ﺇﻥ ﻛﺎﻧﺖ ﻛﻞ ﻭﺍﺣﺪﺓ ﺗﻀﻠﻞ ﺍﻷﺧﺮﻯ
ﻭﺗﻨﻘﺪ ﺃﻋﻤﺎﻟﻬﺎ، ﻓﺈﻥ ﺍﻟﻀﺮﺭ ﺑﻬﺎ ﺣﻴﻨﺌﺬ ﻋﻈﻴﻢ ﻭﺍﻟﻌﻮﺍﻗﺐ ﻭﺧﻴﻤﺔ .
( ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ ﻭﻣﻘﺎﻻﺕ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﺑﻦ ﺑﺎﺯ: /4 134 ).
"Idan Jam'iyoyi (Qungiya) s**a yawaita a cikin kowani irin Kasa
ta musulunci ta daga dalilin alkhairi da taimakekeniya, taimako
akan nagarta da jin tsoron Allah tsakanin musulmai, ba tare da ta
sa6a son zuciyar ma'abotan ta ba (Membobi), tana da alkhairi
da albarka da fa'idoji mai girma. Amma idan ta kasance
kowanne tana 6atar da dayan ta tana ware ayyukan ta, toh irin
wannan a daidai wannan lokaci cutar dake cikin ta mai girma ne
uqubar da masaukin ta".
Da wannan zamu iya fahimtar alkhairin dake cikin kafa Qungiya
domin gudanar da ayyukan addini wajen taimakawa juna. Kuma
babu laifi idan sun sanya wami a matsayin shugaba domin
gudanar da tsare tsaren da ya kamata. Hakan ya tabbata daga
abunda Shaykhul Islam Ibn Taymiyyah (Allah ya masa rahama)
yake cewa:
ﻗﺎﻝ ﺷﻴﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺍﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ ﻓﻲ ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ:
ﺃﻣﺎ ﻟﻔﻆ ))ﺍﻟﺰﻋﻴﻢ (( ؛ ﻓﺈﻧﻪ ﻣﺜﻞ ﻟﻔﻆ ﺍﻟﻜﻔﻴﻞ ﻭﺍﻟﻘﺒﻴﻞ ﻭﺍﻟﻀﻤﻴﻦ، ﻗﺎﻝ ﺗﻌﺎﻟﻰ } : ﻭَﻟِﻤَﻦْ ﺟﺎﺀَ
ﺑِﻪِ ﺣِﻤْﻞُ ﺑَﻌﻴﺮٍ ﻭﺃﻧﺎ ﺑِﻪِ ﺯَﻋﻴﻢٌ { ، ﻓﻤﻦ ﺗﻜﻔﻞ ﺑﺄﻣﺮ ﻃﺎﺋﻔﺔ؛ ﻓﺈﻧﻪ ﻳﻘﺎﻝ: ﻫﻮ ﺯﻋﻴﻢ، ﻓﺈﻥ ﻛﺎﻥ
ﻗﺪ ﺗﻜﻔﻞ ﺑﺨﻴﺮ ﻛﺎﻥ ﻣﺤﻤﻮﺩﺍً ﻋﻠﻰ ﺫﻟﻚ، ﻭﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﺷﺮﺍً ﻛﺎﻥ ﻣﺬﻣﻮﻣﺎً ﻋﻠﻰ ﺫﻟﻚ .
"Amma lafazin "ZA'EEM" (Shugaba), lallai shi kwatankwacin
dandazon Jama'a ne. Allah madaukain Sarki, Yace: {Kuma
wanda ya zo da shi, yana da kayan rakumi daya, kuma ni ne
lamuni game da shi). Duk wanda aka daura masa nauyin
al'amari na wasu mutane (Qungiya), sai ace shine shugaba. Idan
ya kasance haqiqa ya dauki nauyin da alkhairi, sai ya zama abun
yabawa kan haka. Idan ko ya kasance sharri ne, sai ya zama
abun kushewa da zargi kan haka"
Bayan da Sheikhul Islam ya gama bayyana haka, a qarqashin
wannan shine ya qara da wannan maganar duk wake daya yayi
cikin Fatawa nashi. Domin qara da tabbatar da haka, sai ya
cigaba da cewa:
ﻭﺃﻣﺎ )) ﺭﺃﺱ ﺍﻟﺤﺰﺏ (( ؛ ﻓﺈﻧﻪ ﺭﺃﺱ ﺍﻟﻄﺎﺋﻔﺔ ﺍﻟﺘﻰ ﺗﺘﺤﺰﺏ؛ ﺃﻱ: ﺗﺼﻴﺮ ﺣﺰﺑﺎً، ﻓﺈﻥ ﻛﺎﻧﻮﺍ
ﻣﺠﺘﻤﻌﻴﻦ ﻋﻠﻰ ﻣﺎ ﺃﻣﺮ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻪ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ ﻣﻦ ﻏﻴﺮ ﺯﻳﺎﺩﺓ ﻭﻻ ﻧﻘﺼﺎﻥ؛ ﻓﻬﻢ ﻣﺆﻣﻨﻮﻥ، ﻟﻬﻢ ﻣﺎ
ﻟﻬﻢ ﻭﻋﻠﻴﻬﻢ ﻣﺎ ﻋﻠﻴﻬﻢ، ﻭﺇﻥ ﻛﺎﻧﻮﺍ ﻗﺪ ﺯﺍﺩﻭﺍ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻭﻧﻘﺼﻮﺍ ﻣﺜﻞ ﺍﻟﺘﻌﺼﺐ ﻟﻤﻦ ﺩﺧﻞ
ﻓﻲ ﺣﺰﺑﻬﻢ ﺑﺎﻟﺤﻖ ﻭﺍﻟﺒﺎﻃﻞ ﻭﺍﻹﻋﺮﺍﺽ ﻋﻤﻦ ﻟﻢ ﻳﺪﺧﻞ ﻓﻲ ﺣﺰﺑﻬﻢ، ﺳﻮﺍﺀ ﻛﺎﻥ ﻋﻠﻰ
ﺍﻟﺤﻖ ﻭﺍﻟﺒﺎﻃﻞ؛ ﻓﻬﺬﺍ ﻣﻦ ﺍﻟﺘﻔﺮﻕ ﺍﻟﺬﻱ ﺫﻣﻪ ﺍﻟﻠﻪ ﺗﻌﺎﻟﻰ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ، ﻓﺈﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ ﺃﻣﺮﺍ
ﺑﺎﻟﺠﻤﺎﻋﺔ ﻭﺍﻻﺋﺘﻼﻑ، ﻭﻧﻬﻴﺎً ﻋﻦ ﺍﻟﺘﻔﺮﻗﺔ ﻭﺍﻻﺧﺘﻼﻑ، ﻭﺃﻣﺮﺍ ﺑﺎﻟﺘﻌﺎﻭﻥ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺒﺮ ﻭﺍﻟﺘﻘﻮﻯ،
ﻭﻧﻬﻴﺎ ﻋﻦ ﺍﻟﺘﻌﺎﻭﻥ ﻋﻠﻰ ﺍﻹﺛﻢ ﻭﺍﻟﻌﺪﻭﺍﻥ ‏) ‏( 2‏) .
‏( 1 ‏) ﻳﻮﺳﻒ: .72
‏( 2 ‏) * )) ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ (( ‏( / 11 92 )
"Dangane da Jagorancin Qungiya, jagorancin al'ummah wacce
take gungiyantuwa, ma'ana ta zama wata Qungiya. Idan sun
kasance sun hadu ne kan abunda Allah da Manzon sa s**a yi
umurni dashi ba tare da yin qari ko ragi ba, su muminai ne.
Abunda ke nasu nasu ne, abunda ke kan su yana kansu. Idan ko
sun kasance sunyi qari cikin haka, kuma s**a yi ragi, misalin
Ta'assubanci ga wanda ya shiga Qungiyar su da abunda yake
gaskiya ko na 6ata, da juya baya ga wanda bai shiga Qungiyar su
ba, koda ace mai shi ya kasance akan gaskiya da 6ata. To
wannan shine irin Qumgiyacin da Allah madaukakin sarki ya
kushe shi da Manzon sa. Domin Allah da Manzon sa sunyi
umurni ne da Jama'a da hadin kai, da kuma hani game da
rarrabuwa da sa6ani. Kuma yayi umurni da taimakekeniya akam
nagarta da jin tsoron Allah, da hani kan taimakekeniya kan
zunubi da qiyayyah"
Sai Manyan Malaman Sunnah s**e cewa:
ﺃﻣﺎ ﻣﻦ ﺗﺤﺰُّﺏ ﻟﻨﺼﺮﺓ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﻭﺍﻟﺪﻓﺎﻉ ﻋﻨﻪ ﻓﻠﻴﺲ ﺩﺍﺧﻠًﺎ ﻓﻴﻤﻦ ﺫﻣﻬﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﺎﻟﺘﻔﺮﻕ
ﻭﺍﻟﺘﺤﺰﺏ، ﻭﺇﻻ ﺳﻮَّﻳﻨﺎ ﺑﻴﻦ ﺟﻨﺪ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺃﻭﻟﻴﺎﺋﻪ، ﻭﺟﻨﻮﺩ ﺍﻟﺸﻴﻄﺎﻥ ﻭﺃﻭﻟﻴﺎﺋﻬﻢ !
ﺍ. ﻫـ ‏( ﺍﻹﺳﻼﻣﻴﻮﻥ ﻭﺍﻟﻌﻤﻞ ﺍﻟﺴﻴﺎﺳﻲ ﺹ 90 ) .
"Duk wanda s**a yi Qungiya domin taimakon Addini da kariya
gare shi, baya daga cikin wanda Allah ya kushe da rarrabuwa da
Qunguyanci. In ba haka ba zamu daidaita sojojin Allah da
masoyan sa, da kuma sojojin Shaidan da masoyan sa"
Wasun su s**a ce:
ﻭﺍﻟﺮﻣﻲ ﺑﺎﻟﺤﺰﺑﻴﺔ ﺭﻣﻲ ﺑﺎﻟﺒﺎﻃﻞ ﻭﻣﻨﺸﺄﻩ : ﺍﻟﺠﻬﻞ ﺑﻤﻌﻨﻰ ﺍﻟﺤﺰﺑﻴﺔ، ﻓﺄﻱ ﺟﻤﺎﻋﺔ ﺍﺟﺘﻤﻌﻮﺍ
ﻋﻠﻰ ﻧﺼﺮﺓ ﻣﺒﺪﺃ ﻣﺎ، ﻓﻬﻢ ﺣﺰﺏ، ﻓﺈﺫﺍ ﻛﺎﻥ ﺍﻟﻤﺒﺪﺃ ﺍﻟﺬﻱ ﺍﺟﺘﻤﻌﻮﺍ ﻋﻠﻰ ﻧﺼﺮﺗﻪ ﺣﻘًﺎ،
ﻓﺤﺰﺑﻴﺘﻬﻢ ﻣﺤﻤﻮﺩﺓ، ﻭﺇﻻ ﻓﺤﺰﺑﻴﺘﻬﻢ ﻣﺬﻣﻮﻣﺔ، ﻭﺍﻟﻠﻪ ـ ﻋﺰ ﻭﺟﻞ ـ ﻗﺪ ﻣﺪﺡ ﻓﻲ ﺍﻟﻘﺮﺁﻥ
ﺍﻟﻜﺮﻳﻢ ﺣﺰﺏ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻘﺎﻝ : ‏( ﺃُﻭْﻟَﺌِﻚَ ﺣِﺰْﺏُ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺃَﻻ ﺇِﻥَّ ﺣِﺰْﺏَ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﻫُﻢُ ﺍﻟْﻤُﻔْﻠِﺤُﻮﻥَ ‏) ؛
"Jifan da Qungiyanci da jifar qarya da yada shi: Jahiltar ma'anar
Qungiyamci ne. Duk wata Jama'a da ta hadu akan taimako dake
da manufa, su yan Qungiya ne, idan manufar ya kasance wanda
aka hadu ne akan taimakon gaskiya. Toh Qungiyar su abun
yabawa ne. Idan bai zama haka ba, sai ya zama abun kushewa.
Allah madaukakin Sarki haqiqa yayi yabi cikim Qur'ani ga
Qumhiyar Allah, sai Yace: (Wadancan sune Qimgiyar Allah, ku
saurara kuji, lallai Qungiyar Allah sune masu rabauta)"
Ashe kena zalunci mutum yazo yana jifar wata Qungiya da
kalmar Bidi'ntarwa ba tare da yayi la'akari da irin ayyikan su ba,
da kuma irin abunda suke gudanaewa cikim karantarwar su
saboda wata ra'ayi na hassada ko baqin ciki yake da ita
qungiyar. Domin duk Qungiyar da take bisa hanyar daidai ba tare
da kauce wa karantawar Sunnah, ko shakka babu, abun yabawa
ne.
TA'ASSUBANCI KAN WANI MALAMI BAI TA6A MANHAJIN
SALAF BA, QUNGIYANCI NE:
Tabbatarwar gaskiya ne bisa hanyar dacewa domin warware
shubuhar masu da'awar SALAFIYYAH cikin ta'assubanci da
qoqarin kore alkhairan dayawa daga malamai na Sunnah
wadanda s**a jima suna khidimta wa addinin musulunci bisa
karantawan Kitabu Wassunnah, musamman idan akwai sa6anin
fahimta wanda tasha banban da abun da malamin su ya tafi
akan sa. Galibin su zaka ji suna cewa gorgodon yanda malami
wane ya auna wani malami, suma a hakan zasu auna shi. Kuma
duk hakan ya qunshi yanda shi malami ya auna shi a babin yabo,
ko jarraha shi. Abun tambaya anan shine, shin hakan da suke, ya
dace da karantarwan magabata ko a'a? Shin hakan hada kan
al'ummah ne, ko wargaza kan al'ummah? Bari muga me manyan
Malaman Sunnah S**a ce game da wannan irin ta'assubanci
marar anfani:
ﻗﺎﻝ ﺷﻴﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺍﺑﻦ ﺗﻴﻤﻴﺔ – ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ :-
ﻛﺜﻴﺮ ﻣﻦ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻳﺨﺒﺮ ﻋﻦ ﻫﺬﻩ ﺍﻟﻔﺮﻕ ﺑﺤﻜﻢ ﺍﻟﻈﻦ ﻭﺍﻟﻬﻮﻯ ﻓﻴﺠﻌﻞ ﻃﺎﺋﻔﺘﻪ ﻭﺍﻟﻤﻨﺘﺴﺒﺔ
ﺇﻟﻰ ﻣﺘﺒﻮﻋﻪ ﺍﻟﻤﻮﺍﻟﻴﺔ ﻟﻪ ﻫﻢ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻭﺍﻟﺠﻤﺎﻋﺔ ؛ ﻭﻳﺠﻌﻞ ﻣﻦ ﺧﺎﻟﻔﻬﺎ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺒﺪﻉ ﻭﻫﺬﺍ
ﺿﻼﻝ ﻣﺒﻴﻦ . ﻓﺈﻥ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﻖ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ ﻻ ﻳﻜﻮﻥ ﻣﺘﺒﻮﻋﻬﻢ ﺇﻻ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ
ﻭﺳﻠﻢ ﺍﻟﺬﻱ ﻻ ﻳﻨﻄﻖ ﻋﻦ ﺍﻟﻬﻮﻯ ﺇﻥ ﻫﻮ ﺇﻻ ﻭﺣﻲ ﻳﻮﺣﻰ ﻓﻬﻮ ﺍﻟﺬﻱ ﻳﺠﺐ ﺗﺼﺪﻳﻘﻪ ﻓﻲ ﻛﻞ
ﻣﺎ ﺃﺧﺒﺮ ؛
" ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ "
Fassara:
"Shaykhul Islam Ibnu Taymiyyah (Allah ya masa Rahama), Yace:
Dayawa daga mutane, suna labartawa game da wannar Qungiya,
da hukunci na zato da son zuciya, sai su suma sanya gungun
mutane (wata Jama'a), masu dangantuwa zuwa ga bin sa, da
ji6antuwa gare shi, su kuma Ahlssunnah wal Jama'a ne, sai su
sanya duk wanda ya sa6a wa ita Qungiyar tasu cewa ya zama
Dan Bidi'a, wannan 6ata ce mabayyani. Domin lallai su
Ahlusssunah basu da mabiyi face Manzin Allah tsira da amincin
Allah su tabbata gare shi, wamda baya magana bisa son zuciya,
sai idan har wahayi aka masa, shine wanda ya wajaba a gaskata
shi cikin dukkan abunda ya bada labari."
Shaykhul islam bai tsaya nan ba. Ya kuma qara da wannan:
ﻭﻗﺎﻝ ﺃﻳﻀﺎ – ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ ":- ﻓﻼ ﻳﺠﻮﺯ ﻷﺣﺪ ﺃﻥ ﻳﺠﻌﻞ ﺍﻷﺻﻞ ﻓﻲ ﺍﻟﺪﻳﻦ ﻟﺸﺨﺺ ﺇﻻ
ﻟﺮﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻭﻻ ‏[ﻟـ ‏]ﻗﻮﻝ ﺇﻻ ﻟﻜﺘﺎﺏ ﺍﻟﻠﻪ ـ ﻋﺰ ﻭﺟﻞ ـ.
ﻭﻣﻦ ﻧﺼﺐ ﺷﺨﺼﺎ ﻛﺎﺋﻨﺎ ﻣﻦ ﻛﺎﻥ ﻓﻮﺍﻟﻰ ﻭﻋﺎﺩﻯ ﻋﻠﻰ ﻣﻮﺍﻓﻘﺘﻪ ﻓﻲ ﺍﻟﻘﻮﻝ ﻭﺍﻟﻔﻌﻞ ﻓﻬﻮ
} ﻣﻦ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻓﺮﻗﻮﺍ ﺩﻳﻨﻬﻢ ﻭﻛﺎﻧﻮﺍ ﺷﻴﻌﺎ { ﺍﻵﻳﺔ ﻭﺇﺫﺍ ﺗﻔﻘﻪ ﺍﻟﺮﺟﻞ ﻭﺗﺄﺩﺏ ﺑﻄﺮﻳﻘﺔ ﻗﻮﻡ ﻣﻦ
ﺍﻟﻤﺆﻣﻨﻴﻦ ﻣﺜﻞ : ﺍﺗﺒﺎﻉ : ﺍﻷﺋﻤﺔ ﻭﺍﻟﻤﺸﺎﻳﺦ ؛ ﻓﻠﻴﺲ ﻟﻪ ﺃﻥ ﻳﺠﻌﻞ ﻗﺪﻭﺗﻪ ﻭﺃﺻﺤﺎﺑﻪ ﻫﻢ
ﺍﻟﻌﻴﺎﺭ ﻓﻴﻮﺍﻟﻲ ﻣﻦ ﻭﺍﻓﻘﻬﻢ ﻭﻳﻌﺎﺩﻱ ﻣﻦ ﺧﺎﻟﻔﻬﻢ .
ﻓﻴﻨﺒﻐﻲ ﻟﻺﻧﺴﺎﻥ ﺃﻥ ﻳﻌﻮﺩ ﻧﻔﺴﻪ ﺍﻟﺘﻔﻘﻪ ﺍﻟﺒﺎﻃﻦ ﻓﻲ ﻗﻠﺒﻪ ﻭﺍﻟﻌﻤﻞ ﺑﻪ ﻓﻬﺬﺍ ﺯﺍﺟﺮ .
(10): " ﻣﺠﻤﻮﻉ ﺍﻟﻔﺘﺎﻭﻯ 9-8/20)" ).
Fassara:
Ya kuma ce: "Baya halatta ga wani ya sanya asali cikin addini ga
wani mutum face wa Manzon Allah (SAW), ko wani magana face
littafin Allah madaukakin sarki (Qur'ani). Duk wanda ya danganta
wani mutum halittace, wanda yake nuna soyayyah da kuma nuna
qiyayyah kan abunda ya wafaqa cikin magana ko aiki, toh irin
wannan mutumin, {Yana daga cikin wadanda s**a rarraba
addinin su kuma s**a kasance masu 6angarewa} Ayah. Idan
mutumin ya fahimtar, ya kuma ladabtar da wata hanyar mutane
da muminai, Misali: Bin shugabanni da manyan Malamai; toh bai
cancanta ya sanya ikon sa da ma'abotan shi sune s**a fi kowa
ba, har yan dinga nuna soyayyah ga dukkan wanda ya yarda
dasu, da kuma nuna qiyayyah ga dukkan wanda ya sa6a musu.
Saboda haka, abun da yafi dacewa ga mutum shine, ya kimtsa
kansa fahimtar sa 6oyayyah a zuciyar sa da aiki dashi, toh
wannan shine wanda ya wa'azantu"
Saboda haka, babu wani wanda zai zo ya dinga rushe abun da
al'umma suke kai na alkhairi don kawai malamin sa ya sa6a
musu bisa fahimtar sa. Domin aikata hakan, baya daga abunda
magabata na qwarai (SALAF) s**a tafi akan sa. Idan kuma
mutum ya haqiqan ce akan haka, ko shakka babu, ya tabbata
mai tsananin son zuciya da nuna ta'assubanci tsakanin al'umma
masu qoyi kan karantarwan Kitabu. Wassunnah.
Shima wannan kenan a taqaice. Sai a kashi na gaba zamu ga,
shin don malaman sunnah wadanda aka san su, don sun ta6a
yabon wani malami, shike nuna yafi karfin a sa6a masa ko a'a.
Allah ya datar damu bisa hanyar gaskiya
Signed: Motivator & Author Kalimullah Ahmad Hinna
23 hrs · Facebook for Android · Public

08/06/2020

Darasi daga watan Ramadan (9).

Idan ba,a mantaba mun tsaya ne a in da muke kawo wata muhimmiyar Darasi da watan Ramadan ta koyar damu wato na gabatar da salloli na nafila Muna fatan cigaba da wannan aikin har zuwa karshen rayuwarmu.

Mun fara kawo wasu daga Cikin sallolin nafila domin tunatar da bayin Allah akan su kasance masu aikatawa

Yau zamu cigaba.

1) nafilar sallah isha,i.

Hadisi yazo daga Ibn umar cewa yayi sallah nafila tare da manzon allah bayan sallah isha,i raka,a biyu.

Sannan akwai raka,a biyu na nafila kafun sallah isha,i dogaro da hadisin da abdlahi bn mugaffal ya ruwaito na
" بين كل أذانين صلاة"

2) nafilar bayan sallah jumma,a.

Ana gabatar da sallah nafila raka,a biyu bayan sallah jumma,a amma a gida kamar yadda yazo a hadisin Ibn umar

كان (ص) لا يصلي بعد الجمعة حتي ينصرف فيصلي ركعتين في بيته.

3) sallah wutiri.

Ana bukatar a kullun mutun ya ringa gabatar da sallah witiri sannan ya sayata itace sallahrsa ta karshe a wannan dare dalilin fadin manzon Allah

" اجعلوا آخر صلاتكم بالليل وترا"
Ga Wanda zai tashi Cikin dare ya gabatar da qiyamul laili zai jinkirta sallah wutirinsa ga Wanda kuma bazai tashi Cikin dare ba zai iya gaggauta wutirinsa yayita bayan sallah isha,i.

Allah yasa mu dace ya bamu ikon aikatawa

Anas Jibir
16/10/1441.
08/06/2020.

05/06/2020

Darasi daga watan Ramadan (9)

Sallolin Nafila:

A watan ramadan yawancin jama,a mun kasance bama nisantar masallaci hakan yasa salloli na nafilfilu basa wahalar damu

Amma daga lokacin da Ramadan ta fita sai kaga bayin Allah da dama basa iya tsayawa suyi sallah na nafila sai su tsaya iya na farilla

Wannan kuma kuskurene ya kmt yadda mukayi wata munayi ya zama abun yabi jikinmu ta yadda zamu cigaba dashi har karshen rayuwarmu.

Ga kadan daga Cikin sallolin nafila:

1) Raka,atainil fajr

Sune raka,o,i 2 da akayinsu kafun sallah asubah, manzon Allah (saw) yace gamedasu

ركعتا الفجر خير من الدنيا وما فيها
Sunfi duniya da abunda ke cikinta.

2) SALATUD DUHA:

sune raka,o,in da ake yinsu a lokacin duha (hantsi) kafun zawali.

Manzon Allah yace kowace gaba ajikin Dan Adam yana wayar gari akwai sadaka akanta wato akwai sadaka 360 akan kowa sai yace

و يجزي من ذالك ركعتان يركعهما من الضحي
Yin raka,o,i guda 2 na duha yana wadatar dasu.

3) nafilan sallah azahar

Manzon Allah ya kasance yana yin sallah raka,o,i guda 2 kafun sallah azahar da bayan sallah azahar kamar yadda yazo a ruwayar Ibn umar

a ruwayar nana Aisha kuma raka,a hudu kafun sallah azhar.

Sannan manzon Allah yace

من حافظ علي اربع ركعات قبل الظهر واربع بعضها، حرمه الله علي النار.
Duk Wanda ya kiyaye sallah raka,a 4 kafun azahar da raka,a 4 a bayanta Allah zai haramtashi daga shiga wuta.

4) nafilar sallah la,asar

Manzon Allah ya kasance yana sallah raka,a 4 kafun sallah la,asar yana rabe tsakaninsu da sallama. Sannan yace gamedasu

رحم الله امرأ صلي قبل العصر اربعا
Allah yayi rahama ga mutumin da yake sallatan raka,a 4 kafun sallah la,asar.

5) nafilar sallar magriba.

Manzon Allah ya kasance yana sallatar raka,o,i guda 2 bayan sallah magriba. Sannan a wata ruwayar manzon Allah yace kuyi sallah (nafila) kafun magriba har sau uku sannan yace ga Wanda yaso.

Wannan ya nuna Wanda ya samu dama zai iya sallah nafila kafun magriba amma bayan faduwar.

Allah yasa mu dace

Anas Jibir.
14/10/1441
05/06/202

04/06/2020

Darasi daga watan Ramadan (8).

QIYAMUL LAILI (TSAYUWAR DARE)

A watan ramadana bayin Allah da dama sun dukufa wajen gabatar da ibada na tsayuwar dare domin cin ribar hadisin manzon Allah dayace

من قام رمضان ايمانا واحتسابا غفر له ما تقدم من ذنبه

Saboda wannan mafi yawan bayin Allah s**a dukufa wajen gabatar da ibadar qiyamul laili a watan Ramadan hakan yasa watar tana fita sai s**a dena

Shi qiyamul laili ibadace mai matukar falala Wanda yake da dukkan alkhairi duniya da lahira, Kuma bawai sai a watan Ramadan kawai akeyinta ba, anayinta a kowace wata daga Cikin watanni.

Ga kadan daga Cikin falalar ta:

1) Manzon Allah ya tsawatar gameda barinta a in da yake cewa :

"يا عبد الله لا تكن مثل فلان : كان يقوم الليل فترك قيام الليل"
Karka zama kamar wane: Wanda yana tashi Cikin dare amma baya gabatar da qiyamul laili.

2) qiyamul laili aikin manzon Allah ne kamar yadda Nana Aisha ta ruwaito cewa har dunduniyarsa yana yagewa saboda tsayuwa.

" كان النبي ص يقوم من الليل حتي تتفرط قدماه "

3) shedan yayi fitsari a kunnen wanda ya barta

An tambayi manzon Allah gameda Wanda ya kwanta bacci bai farka yayita har asubah sai yace

" ذاك رجل بال الشيطان في اذنيه"
Shedan ya masa fitsari a kunnensa.

4) Tana zama dalilin shigarda bawa aljannah.

Manzon Allah yace

أيها الناس افشو السلام، واطعموا الطعام، وصلوا بالليل والناس نيام، تدخلوا الجنة بسلام"
Daga Cikin ayyukan da zasu sa mutun ya shiga aljannah da aminci saiya lissafa harda tsayuwar dare.

5) mafificin sallah bayan sallah farillah itace sallar dare.

Manzon Allah yace:

افضل الصلاة بعد الفريضة صلاة الليل
Mafificin sallah bayan na farilla shine sallah dare.

6) mai yinta Allah ya tanadar masa da benayi a gidan aljannah.

Manzon Allah yace acikin aljannah akwai wasu benaye Wanda na waje yana ganin na ciki hakanan na ciki yana ganin na waje, sai sahabbai s**a tmby shi, saiya lissafa wasu ayyukan da bawa zaiyi ya samu wannan gidan daga ciki akwai tsayuwar dare.

Allah yasa mu dace.

Anas Jibir
13/10/1441.
04/06/2020

01/06/2020

Darasi daga watan Ramadan (7).

Idan ba,a manta ba Muna Cikin bayani akan ladabtarwa da watan Ramadan tamana na yawaita karatun alqur,ani mai girma.

Shi karatun alqur,ani ana bukatar musulmi ya zama yana yawaita aikatawa a kowace rana sannan akowace wata bawai sai watan Ramadan ba.

Karatun alqur,ani yanada falala masu tarin yawa daga cikinsu akwai:

1) QUR,ANI ZAI CECE MASU KARANTASHI A RANAR ALQIYAMA

manzon Allah saw yace:

"اقاوا القران فانه ياتي يوم القيامة شفيعا لاصحابه "

Ku karanta alqurani domin zaizo ranar tashin alqiyama yana ceton ma,abotansa.

2) MAFI ALKHAIRI SHINE WANDA YA KARANTASHI KUMA YA KARANTAR DA WASU.

manzon Allah saw yace :

"خيركم من تعلم القران وعلمه "

3) DUK WANDA YA KARANTA ALQUR,ANI ALLAH ZAI BASHI LADA GOMA AKAN KOWANI HARAFI DAYA KARANTA.

manzon Allah saw yace :

" من قرا حرفا من كتاب الله فله حسنة، والحسنة بعشر أمثالها "

4) WANDA YAFI KOWA YAWAN BENAYE AGIDAN ALJANNAH SHINE WANDA YA FI YAWAN HADDAN AYOYIN ALQUR,ANI.

Manzon Allah yace :

" يقال لصاحب القران : اقرا وارتق ورتل كما كنت ترتل في الدنيا ، فان منزلتك عند آخر آية تقروها"

Allah ya bamu ikon karantawa akowace rana sannan yasa qurani ya cecemu.

Anas Jibir.
09/10/1441.
01/06/2020.

31/05/2020

Darasi daga watan Ramadan (6).

YAWAITA KARATUN ALQUR,ANI MAI GIRMA.

A watan Ramadan bayin Allah da dama sun dukufa wajen yawaita karantawa da kuma sauke alqur,ani mai girma.

Acikin watar kawai zakaji mutun yana cewa ya sauke sau 1 ko 2 ko 3 ko 4 ko 5 koma samada hakan. Sannan Irina kananan dalibai muma Muna yawaita kara tawa gwargwadon karatun mu.

Amma abun mamaki daga lokacin da Ramadan ya fita sai kaga yawanci an koma gidan jiya anyi watsi ko kuma ince an rage karatun da ake gabatarwa a Ramadan wasu kanma denawa sukeyi gaba daya.

Wannan kuma ba karamin kuskure bane muyi kokari kar mu zama bayin Ramadan, domin Allah da muke bautawa a Ramadan shine dai Allah sauran watanni musulunci gaba daya

Kuskurene babba ace baka karatun alqur,ani sai watan ramadan tazo nanm tana fita shi kenan ka ajiyeta.

Wasu ma karatun alqur,anin ma basu iya ba hakan yasa bazaka taba ganinsu da alqur,ani ba kuma sunki suje mkrt a koyar dasu.

Watan Ramadan ta ladavtar damu da yawaita karanta alqur,ani da kuma Neman iliminta da bincike domin sanin ma,anonin dake cikinta

Akwai bukatar muyi amfani da wannan ladabtarwa mu ribaci lokutanmu ta hanyar karanta littafin Allah domin samun tsira duniya da lahira.

Insha Allahu a kashi na (7) zamu kawo falalar karanta alqur,ani mai girma domin kwadaitar da kanmu da masu bibiyarmu ga muhimmancin karanta alqur,ni mai girma.

Allah ya taimakemu ya kuma anfanar damu daga abunda muka karantawa ko saurarawa

Anas Jibir
08/10/1441.
31/05/2020.

30/05/2020

Darasi daga watan Ramadan (5).

Idan ba,a manta ba Muna Cikin lissafo azimummuka na nafila Wanda ya kamata ace bayan watan Ramadan suma Muna azumtarsu domin samun tsira gobe kiyama

Ayyukan tadau,wi,i dai sune suke cike duk in da aka samu gibi a ayyukan bawa na farilla.

Ga wasu daga Cikin ayyukan bayan ukun Dana lissafa.

1: AZUMIN RANAKUN ALKHAMIS DA LITININ.

an tambayi manzon Allah gameda azumin ranar litinin sai yace:

"ذالك يوم ولدت فيه، ويوم بعثت، ....."
Ma,ana manzon Allah yace a ranar litinin aka haifeni kuma ranar aka aikoni

Sannan manzon Allah ya sake cewa:

تعرض الاعمال يوم الاثنين والخميس، فاحب ان تعرض عملي وانا صاام.
Ana bijiro da ayyukan akowace ranar litinin sa alhamis, ni kuma inason a bijiro da aikina ina mai azumi.

Da wannan zamu fahimci cewa abun sone ga musulmi daya ringa azumtar wadanndan ranaku.

2: AZUMI UKU AKOWACE WATA.

Ana son musulmi daya dinga gabatar da azumi uku a kowace wata mafi falalar kuma ya azumceta a kwanakin 13, 14 da 15.

Manzon Allah yace gameda wannan azumin :

صوم ثلاثة ايام من كل شهر صوم الدهر كله

Azumi uku a kowace wata, kamar azumin shekara ne gaba daya.

3: AZUMIN TASU,A DA ASHURA,

Tasu,a da ashura sune ranakun 9 da 10 ga watan almuharram suma ana son gabatar da azumi a wadannan ranaku domin fadin manzon Allah da aka tmby shi gameda azumtarsu sai yace

يكغر السنة الماضية
Azumin ashura yana kankare zunubin shekarar data shude.

4: AZUMI A WATAN SHA,ABAN

Watan sha,aban itace wata ta takwas a calendar Islam. Kuma ita ma ana son a yawaita azumi acikin domin fadin Nana Aisha

لم يكن النبي (ص) يصوم من شهر اكثر من شعبان

Allah ya bamu ikon azumtarsu

Anas Jibir
7/10/1441
30/5/2020

Address

Pawo
Gombe

Telephone

+2348145788615

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Anas kwami posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share