Jikamshi political youths forum

Jikamshi political youths forum Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jikamshi political youths forum, Political organisation, Jikamshi.

A Madadin 'Ya'yan wannan kungiya mai suna a sama da Alummar wannan gari namu mai Albarka.Muna taya mutane uku na garin J...
05/02/2025

A Madadin 'Ya'yan wannan kungiya mai suna a sama da Alummar wannan gari namu mai Albarka.

Muna taya mutane uku na garin Jikamshi murnar samun aikin Fire service a Federal government a karkashin jagorancin Mai girma Dan majalissar tarayya mai wakiltar karamar Hukumar Musawa da Matazu Hon. Abdullahi Aliyu Ahmed Musawa Dujiman katsina.

1- Muhammad Ibrahim Jikamshi
2- Zaidu Garba Tela Jikamshi
3- Nura Yusuf Jikamshi

Muna tayasu Addu'ar Allah ubangiji ya basu ikon sauke wannan nauhi lafiya Allah ya basu ikon ciyar da Alumma gaba da taimakon musulunci da musulmai.

Daga karshe muna Masu fatan alkhairi da fatan zasu rike Aikin su cikin gaskiya da rikon Amana da jajircewa wajan yin aiki ta kuru domin tabbatar da cigaban gari da karamar Hukumar mu da jaharmu da kasa baki daya.

Mai girma DUJIMAN KATSINA irin wannan Aikin alherin ba yau kasoma ba mun Saba ganinshi, muna maka Addu'ar Allah ubangiji ya cigaba da Baka dama da ikon cigaba da taimakon Alumma kamar yadda kasaba.
Allah ya shiga lamuranka ya iya maka duk abunda baka iyawa alfarmar Annabi da Alqura'ni Amin 🤲

✍️

05/02/2025

Mai girma Dan majalissar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Musawa da matazu Hon. Abdullahi Aliyu Ahmed Musawa (Duji...
05/02/2025

Mai girma Dan majalissar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Musawa da matazu Hon. Abdullahi Aliyu Ahmed Musawa (Dujiman katsina) ya sake gwangwaje wasu matasa na mazabar Musawa da matazu su 18 da offer a Federal government ta Aikin Fire service.

Hakan ya biyo bayan wasu matasan daya Samar ma wannan Aikin a watan December da ya gabata na wannan shekara 2024 su (22).

Wannan ba bakon Abu bane a gurin mai girma DUJIMAN KATSINA domin ya Samar ma matasa da yawa aiyuka daban-daban a bangarori kamar haka:

Army, Police, Immigration, Fire service, Civil Defences, Prison Service (Corruptional) Lectures, Health, Federal Medical centre, Federal Teaching Hospital Katsina, da sauran su.

A wata zantawa da mai girma DUJIMAN KATSINA ya yi da manema labarai ya tabbatar da cewa irin wannan Abun alkhairin ya dingayin shi kenan domin ganin ya rage ma matasa zaman banza a yankin Musawa da matazu dama Jahar Katsina baki daya.

Haza zalika ya tabbatar da cewa mutanen da zasufi kowa amfana da irin wadannan offofi nashi zasu kasance talakawane ko marayu wadanda s**ayi karatu kuma basuda abunyi da kuma wadanda basusan minene romon damakaradiya ba a siyasance.

Daga karshe ya sa ma wadannan matasa Albarka acikin Aikin su tare da yimasu Addu'ar Allah ubangiji ya basu ikon sauke nauhin da Allah ya Daura Masu lafiya, haka zalika ya gargadesu dasu rike Aikin su da matukar muhimmanchin gaske duba da yadda s**aga lamarin Samun aiki yazama a wannan zamanin da muke ciki.

Rahoto
✍️

5/02/2025

A madadin 'Ya'yan kungiyar   na taya dan takarar Counsilor na Jikamshi ward Hon. Haruna Magaji murnar karbar tutar yakin...
02/02/2025

A madadin 'Ya'yan kungiyar na taya dan takarar Counsilor na Jikamshi ward Hon. Haruna Magaji murnar karbar tutar yakin neman zame a karkashin Jam'iyar APC.

Hon. Haruna Magaji ubangiji Allah yasa Alkhairi Allah ubangiji ya baka ikon kamanta gaskiya acikin shugabancin ka Àmin

✍️

'Yan Takarar Kansiloli Na Jam'iyyar Apc Na Karamar Hukumar Musawa, A Jihar Katsina Sun Amshi Tutar Shiga Yakin Neman Zab...
02/02/2025

'Yan Takarar Kansiloli Na Jam'iyyar Apc Na Karamar Hukumar Musawa, A Jihar Katsina Sun Amshi Tutar Shiga Yakin Neman Zabe.

A ranar lahadi 2/2/2025, Dan majalisar tarayya mai wakiltar Musawa/ Matazu Hon. Abdullahi Aliyu Janaral tare da Dan takarar shugaban karamar hukumar Hon. Aliyu Idris Gingin su ka mika tuta ga 'yan takarar kansilolin na mazabu 11 na karamar hukumar, yayin kaddamar da gangamin yakin zabe.

Mataimakin shugaban Jam'iyyar Apc na Jihar Katsina Alhaji Bala Abubakar Musawa (Cigarin Musawa) a jawabin da ya gabatar yayin kadda mar da gangamin yakin neman zaben tare da bada tuta ga yan takarar Kansilolin ya bayyana irin yadda su ka ida kakkabe Jam'iyyun adawa a karamar hukumar musamman Jam'iyyar PDP.

Yayin kaddamar da gangamin yakin neman zaben an bayyana manya, manyan Jiga -Jigan Jam'iyyar PDP da su ka canza sheka su ka dawo cikin Jam'iyyar Apc, daga cikinsu akwai Hon. Sada Abdullahi Inde tsohon Dan takarar Dan majalisar tarayya mai wakiltar Musawa da Matazu, tsohon shugaban karamar hukumar Musawa Hon. Tanimu Isma'il Kira. Da dai sauransu.

A jawaban da su ka gabatar a lokacin taron gangamin yakin neman zaben, sun bayyana cewa salon yadda Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda yake tafiyar da mulkin Jihar Katsina yasa su ka gamsu da tafiyar su ka dawo Jam'iyyar Apc domin suma bada gudumuwarsu ga ciyar da Jihar nan gaba.

Mutane da dama ne su ka tofa albarcin bakin su, a wajen taron, wanda su ka hada da Hon. Salisu Hamza Rimaye Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Kankia, Hon. Aminu Garba (Sai Baba) Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Danmusa, Hon. Lawal H. Yaro Away Dan majalisa mai wakiltar karamar Hukumar Musawa, sun bayyana yadda su ka kashe Jam'iyyar adawa a yankunansu.

Sauran manyan mutanen da su ka halarci taron sun hada da Dan takarar shugaban karamar hukumar Jibia Hon. Surajo Ado Jibia, sai Dan takarar shugaban karamar hukumar Danmusa Hon. Ibrahim Namama Maidabino, Hon.Hassan Kawari ma'ajin Jam'iyyar Apc na Jiha, Hon. Nasiru.

Baya gajiya da aikin alkhari a kowane lokachi AG Alh. Nura Tela Jikamshi, Ya kawo sabon gini da sabon Mono (Borehole) a ...
02/02/2025

Baya gajiya da aikin alkhari a kowane lokachi AG Alh. Nura Tela Jikamshi, Ya kawo sabon gini da sabon Mono (Borehole) a Makarantar Mallamawa Primary School, Sabon Garin Jikamshi, Sannan yau ma an cika Masu azuzuwa da kujerun zama, Kalkashin Jagoranchi Mal. Auwal Shuaibu Tela,

Alumma nagodiya, da samun irinka a wannan yanki namu, Allah Ubangiji Yakara shiga Lamarinka, Yakara tsaremana Kai Allahumma Amen 🤲🙏

Ƴan Takarar Shugabancin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina Na Jam’iyyar APC Sun Karɓi Tutar Yaƙin Neman ZaɓeA ranar Lahadi ...
26/01/2025

Ƴan Takarar Shugabancin Ƙananan Hukumomin Jihar Katsina Na Jam’iyyar APC Sun Karɓi Tutar Yaƙin Neman Zaɓe

A ranar Lahadi 26 ga watan Janairun 2025, Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, tare da shugaban jam'iyyar APC na ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, s**a jagoranci ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi na jam’iyyar APC, tare da miƙa masu tutar takara a ƙaramar hukumar Ingawa.

Bayan miƙa tutocin yaƙin neman zaɓen an kuma amshi ƴan Jam'iyyun adawa sama da mutum 40,000 wanda s**a dawo jam'iyyar APC.

Da yake magana shugaban jam'iyyar APC ta ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana jin daɗin shi ganin yadda jam'iyyar ta APC a jihar Katsina take tsintsiya ma ɗaurin ki ɗaya, ya kuma ce dukkanin masu faɗa aji a siyasar jihar Katsina suna cikin jami'yyar APC hakan yana daga cikin nasabar rushewar jam'iyyun adawa a Katsina.

Ya kuma ƙarada jam'iyyar APC zata lashe zaɓukan ƙananan hukumomin jihar Katsina baki ɗaya duba da irin ƙoƙarin gwamnan jihar Malam Dikko Umaru Radda, ya kuma yi kira ga dukkanin ƴan jam'iyyar APC da kada su nuna wariya ko bambanci ga sabbin wanda s**a shigo jam'iyyar ta APC.

Bayan miƙa tutocin yaƙin neman zaɓen gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya fara da yima ɗumbin ƴan jam'iyyar adawa da s**a dawo jam'iyyar APC barka da zuwa jam'iyyar adalci kuma jam'iyya mai taimakon al'umma.

Ya kuma cigaba da cewa jam'iyyar APC a jihar Katsina tana nan zama daram dam, itace jiya itace yau kuma itace gobe, kuma bata jin tsoron yin takara ko shiga zaɓe da kowace jam'iyya idan sun shirya mun shirya.

Daga ƙarshe ya yi kira ga ƴaƴan jami'yyar APC da su fito ƙwai da kwarkwata domin zaɓar jam'iyyar APC, sabo da babu rumfar da baza akai akwati ba domin gudanar da sahihin zaɓe.

Cikin manyan mutanen da s**a halarci taron akwai mataimkakin gwamnan jihar Hon. Faruk Lawal Joɓe, tsohon gwamnan jihar Katsina Barr. Ibrahim Shehu Shema, mai taimaka ma shugaban ƙasa kan harkokin siyasa Alh. Ibrahim Masari, ɗaukacin su.

26/01/2025

Somin tabi daga karamar hukumar Ingawa wajen bada tutoci ga 'Yan takara na Jamm'iyar APC na shugabancin Kananan Hukumomi 34 dake jihar Katsina

Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, tsoffin Gwamnonin Jihar Katsina Masari da Shema sun halarci taron masu ruwa da ts...
25/01/2025

Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, tsoffin Gwamnonin Jihar Katsina Masari da Shema sun halarci taron masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar Apc akan zaben kananan hukumomi dake tafe a Jihar Katsina.

A ranar asabar 25/1/2025, Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya jagoranci taron masu ruwa da tsakin na Jam'iyyar Apc akan zaben kananan hukumomin Jihar dake tafe ranar 15/2/2025.

Taron masu ruwa da tsaki ya samu halartar manya, manyan shugabannin Jam'iyyar Apc a Jihar Katsina, Wanda su ka hada da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Tsohon Gwamnan Jihar Katsina Rt. Hon. Aminu Bello Masari, tsohon Gwamna Barr. Ibrahim Shehu Shema, Alh. Dahiru Bara'u Mangal, Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Hon. Faruk Lawal Jobe.

Shugaban Jam'iyyar Apc na Jihar Katsina Alh. Muhammad Sani Ali, mataimakinaa Alh. Bala Abubakar Musawa, Mai baiwa shugaban kasa akan harkokin siyasa Alh. Ibrahim Kabir Masari, Sanata Abu Ibrahim, Col. Abdulmuminu Aminu Mai ritaya.

Tsoffin mataimakan Gwamnan Jihar Katsina Qs. Mannir Yakubu, Barr. Surajo Dan Yaro Damari, Barr. Abdullahi Garba kuma sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Ministoci da su ka fito daga Jihar Katsina Arc. Ahmed Musa Dangiwa, da Hannatu Musa Musawa.

Sanatocin Jihar Katsina masu ci na shiyyar Katsina, Daura da Funtua, yan majalisar tarayya 12 na Jam'iyyar Apc, yan majalisar Dokoki ta Jihar Katsina su 34, yan majalisar zartarwa na Jiha. Da sauran manyan 'yayan Jam'iyyar Apc daga ko'ina a fadin Jihar baki daya.


25th, January, 2025

A yau Juma'a 24 ga watan Janairun 2025, Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya tarbi wasu ƙusoshi na ...
24/01/2025

A yau Juma'a 24 ga watan Janairun 2025, Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya tarbi wasu ƙusoshi na jam'iyyar APC a gidan gwamnatin jihar Katsina, gabannin taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar ta APC a gobe Asabar.

Cikin wanda ya tarba ɗin akwai ministan gidaje da raya birane Arc Ahmad Musa Dangiwa, tsohon sanatan shiyyar Funtua Sanata Bello Mandiya, Sanatan shiyyar Funtua Sanata Muntari Dandutse, Ɗan majalissar tarayya mai wakiltar Musawa da Matazu Hon. Abdullahi Aliyu (Dujiman Katsina).

Rahoto

24/01/2025

Labari Cikin Hotuna!Yadda Gwamna jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, yayi wani zama na musamman da ƴan takara...
24/01/2025

Labari Cikin Hotuna!

Yadda Gwamna jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, yayi wani zama na musamman da ƴan takarar shugabancin ƙananan hukumomi 34 na jihar Katsina, a ƙarƙashin tutar jam'iyyar APC a gidan gwamnatin jihar Katsina, a ranar Laraba 22 ga watan Janairun 2025.

Ganawar tasu na da alƙa da yadda za'a tunkari zaɓen ƙananan hukumomin jihar da ke ƙaratowa.

Cikin waɗan da s**a halarci zaman akwai mataimkakin gwamnan Hon. Faruk Lawal Joɓe, shugaban ma'aikatan gidan gwamnati Hon. Abdulkadir Mamman Nasir, sakataren gwamnan Hon. Abdullahi Aliyu Turaji, da kuma kwamishinan ƙananan hukumomi da masarautu Hon. Bishir Tanimu.

Address

Jikamshi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jikamshi political youths forum posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share