03/09/2026
ABUN BURGEWA: DALIBAN JIHAR KANO DA KE KARATU A SHARDA UNIVERSITY, INDIA, SUN GABATAR DA MAULUDIN ANNABI ﷺ
Greater Noida, India: Daliban Jihar Kano da ke karatu a Sharda University, India, sun gudanar da wani babban taron Maulidin Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam ﷺ a Babban Dakin Taro na Nalanda Premium Hostel, Knowledge Park III, Greater Noida, India.
An fara taron da addu’a da karatun Alƙur’ani Mai Girma, sannan aka gabatar da karatuttuka daban-daban da s**a shafi rayuwa, Sīra da kyawawan ɗabi’un Manzon Allah ﷺ daga bakin malamai da dama.
Daga cikin malaman da s**a gabatar da karatuttuka akwai Sheikh Malam Ibrahim Shira, Sheikh Malam Alawee, Gwani Malam Amir Adnan, da sauran malamai.
Haka kuma, an gabatar da Ta’aliki daga bakin Malam Suhaibu, Gwani Muhammad M. Said, M. Hassan Na Manzon Allah ﷺ, da sauran malamai na gida da na waje.
Karatun Tahni’a da Kasidar Manzon Allah ﷺ
An gabatar da Karatun Tahni’a daga bakin Malam Mannir Bello Dawakin Kudu, sannan aka gabatar da kasidar Manzon Allah ﷺ daga bakin Malam Zahraddin Umar Danbatta (Dagaci).
Taron ya samu halartar Mai Martaba Sarkin Hausawan Sharda University, Cmrd. Sani Ahmad Sa’id, tare da ɗaukacin daliban Jihar Kano da sauran al’ummar Musulmi daga yankin Greater Noida, India.
A ƙarshe, an gudanar da addu’o’in neman nasara da fatan alheri ga ɗaukacin al’ummar Musulmi, tare da addu’ar samun zaman lafiya a Jihar Kano, Najeriya da kuma sauran al’ummar Musulmi a faɗin duniya.
Taron ya kasance wata dama ta ƙara tunawa da rayuwar Manzon Allah ﷺ, ƙaunarsa da kyawawan koyarwarsa, tare da ƙarfafa zumunci da haɗin kai tsakanin ɗalibai da al’ummar Musulmi.
Majiyar Rahoto: Mannir Bello Dawaki