08/03/2022
Assalamu alaikum warahmatullah
Barkanmu da warhaka dafatan Kowa yana lafiya ameen.
Kamar yadda na tuntubi wasu daga cikinmu wasu kuma kwatam sun tsinci Kansu a wannan group, munyi nazari kuma munyi duba da cancantanta da kuna jajircewar da kuke da ita shiyasa muka zaboku domin kasancewa a wannan tafiyar ta SHEIKH DR. IBRAHIM KHALIL a matsayin matasa masu tallan manufofin takarar Malam a matsayin Gwamnan Kano a 2023.
A wannan tafiyar tamu zamuyi tsarin shugabanci nan bada dadewa ba kuma muna Neman goyon baya da hadinkai tareda shawarwarinku domin samun nasarar wannan tafiya mai albarka.
Haka kuma, Insha Allah zamu kasance masu jin shawara da gamsar daku a kowanne lokaci.
Allah yayi mana jagora Ameen.