17/01/2026
Kungiyar Kano Progressive Media Network (KAPMEN) ta jaddada aniyarta ta ci gaba da tallata kyawawan manufofi da nasarorin da DSP Senator Barau I. Jibrin (Maliya) ya shimfiɗa, tare da haskaka ayyukan alherin da ya aiwatar a Kano ta Arewa, cikin ladabi, gaskiya da mutunta kowa.
Kungiyar ta bayyana cewa a siyasa, magana mai tsafta, hujja da gaskiya ita ce tubalin nasara, tare da nuna cikakken yakini cewa ayyukan da Sanata Barau ya aiwatar su ne ginshiƙan da ke haskaka tafiyarsa da karfafa amincewar al’umma a gare shi.
Sanata Barau ya yi fice wajen gudanar da ayyuka na zahiri da s**a shafi tallafa wa al’umma, samar da muhimman ayyukan more rayuwa, da kuma inganta jin dadin jama’a a dukkan yankunan da yake wakilta. Wadannan ayyuka su ne hujjoji karara da ke nuna jajircewarsa, hangen nesansa da kuma kishinsa ga cigaban Jihar Kano.
Kungiyar KAPMEN ta bayyana cikakkiyar gamsuwa da salon jagorancin Sanata Barau, tare da nuna kyakkyawan fata da yakini cewa, da ikon Allah, tafiyar siyasar shekarar 2027 za ta kasance ta nasara. Haka kuma, kungiyar ta jaddada cewa siyasa mai nutsuwa, gaskiya da tsabta na bai wa al’umma damar fahimtar nagarta da kuma zabar abin da ya fi dacewa da muradunsu.
A shekarar 2027, da yardar Allah, za a fuskanci zaɓe cikin kwanciyar hankali, haɗin kai da amincewa, bisa tabbacin cewa nagarta ba ta ɓoyuwa. Kungiyar za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen wayar da kan al’umma kan ayyukan da Sanata Barau I. Jibrin ya aiwatar, domin bambance wanda ya yi aiki a zahiri da wanda ya tsaya kan alkawari kawai.
Allah Ya tabbatar da nasara, Ya kuma sa wannan buri ya cika cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Auwal Wadata Sansan
KAPMEN
Kano North