SO HANA GANIN LAIFI.

SO HANA GANIN LAIFI. C

24/12/2024
09/12/2023

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Adamu Muhammad Adamu Zg, Dibal Sura, Jazuli Umar, Ahmad Muhammad, Huzaifa G. Adam

20/08/2023

Adalilin so..

03/07/2023
03/07/2023

Salami alaykum jama'ar wannan gida Mai Albarka,muna sanar da jama'a littafin A DALILIN SO Za'a dinga yin recoding videos ne na littafin page by page sai a hada da hakuri a dinga karantawa a haka sbd wlh ba lokacin typing din Munyi iya kokarinmu a dinga yin typing din da anfara Kuma abin ya gagara,dafatan za'ayi Mana afuwa👋

ALLAH ÆŠAYA GARI BANBAN (2)HIKAYAR ABDULLAHI MASUNCI DA ABDULLAHI ÆŠANRUWAMasunci bai gushe ba, tsawon kwanaki arba'in, ya...
01/06/2023

ALLAH ÆŠAYA GARI BANBAN (2)

HIKAYAR ABDULLAHI MASUNCI DA ABDULLAHI ÆŠANRUWA

Masunci bai gushe ba, tsawon kwanaki arba'in, yana zuwa bakin teku kullum, tun hudowar rana har faɗuwarta, amma Allah bai nufe shi da k**a kifi ko ɗaya ba. Kuma kullum sai mai gurasa ya ba shi gurasa da nusufi goma na cefane ba tare da ya taɓa canja masa fuska ko ya tambaye shi kifi ba. Bai kuma taɓa ƙyale shi yana jira k**ar yadda yakan yi wa sauran mutane ba.

Duk lokacin da Masunci ya ce masa, "Lissafa abin da kake bi na, mu gani." Sai mai gurasa ya ce, "Bari sai sadda Allah ya h**e maka mu lissafa duka." Idan Masunci ya ji haka sai ya yi ta gode masa, bisa ga wannan karimci. Ya kasance yana sanya masa albarka duk lokacin da zai wuce gida.

A kwana na arba'in da É—aya Abdullahi ya ce wa matarsa, "Ni kam na yi nufin tsinka wannan koma, ko na huta wa kaina da wahalar duniya!"

Matar ta tambaye shi cikin mamaki, "Don me za ka aikata wannan É—anyen aiki?"

Masunci ya ce, "Saboda ga dukkan alamu rabona ya ƙare a cikin wannan sana'a ta kamun kifi. Har yaushe zan daina jin kunyar mai gurasa bisa ga bashin da yake ɗibga mini kullum. Ni kam ba zan ƙara zuwa teku ba, ballantana har na bi ta gaban rumfarsa ya gan ni, tun da babu wata hanya sai ta nan. Duk sadda ya ƙyalla idonsa ya gan ni, sai ya kira ni ya ba ni gurasa da nusufi goma. Ba zai yiwu na ci gaba da karɓar bashinsa ba."

Matar ta ce, "Ai sai ka gode wa Allah da ya sanya soyayyarka cikin zuciyar mai gurasa, ga shi muna samun abinci ta hannunsa kullum. Allah da ya toshe maka hanyar samu daga teku, sai ya buÉ—e maka wata hanyar abinci ta hannun mai gurasa, to mene ne aibu ga wannan?"

Masunci ya ce, "Na tara kuÉ—insa da yawa a kaina, ta yaya zan biya shi idan ya nemi abinsa?"

Matar ta ce, "Ya taɓa tambayarka ne, ko ya taɓa yi maka wata baƙar magana?"

Masunci ya amsa, "Wallahi ko ɗaya, duk ma sadda na ce ya lissafa abin da yake bi na, sai ya ƙi, ya ce sai sadda Allah ya h**e mani."

Matar ta ce, "To, ka gani, kada ka dami kanka. Idan har ya gaj

24/05/2023

ALLAH ÆŠAYA GARI BANBAN

HIKAYAR ABDULLAHI MASUNCI DA ABDULLAHI ÆŠANRUWA

SHIMFIÆŠA

Talaka ne da bai mallaki komai ba a duniya sai 'yar komarsa ta kamun kifi, da ita yake ci ya kuma ciyar da iyalinsa kullum. Yana da mata ɗaya da 'ya'ya tara. Ranar da aka haifa masa jariri na goma sai ya yi wani suɓul-da-baka, abin da ya jawo masa yin kwana arba'in ba tare da ya k**a ko kwaɗo a cikin komarsa ba. A kwana na arba'in da ɗaya ya yi nufin tsittsinka komar don haushi, matarsa ta yi ta ƙarfafa masa gwiwa ha ta shawo kansa ya haƙura, ya saɓa komarsa ya koma bakin teku. A wannan rana kuwa ya yi babban kamu, domin kuwa ya kamo ɗanruwa. S**a yi aminci da ɗanruwan nan wanda har ya gayyace shi zuwa gidansa da ke ƙarƙashin teku.

A cikin wannan hikaya, za mu bi Abdullahi Masunci da abokinsa Abdullahi Ɗanruwa, zuwa ƙarƙashin teku domin ganin irin abubuwan mamaki da ke cikin ruwa da kuma yadda halittun ruwa ke gudanar da rayuwarsy. An dai ce, ALLAH ƊAYA GARI BANBAN.

Ku kasance tare da mu ranar Asabar mai zuwa, inda za mu fara warware muku tabarmar wannan shimfiÉ—a, in sha Allah.

Bukar Mada
24/05/2023

ADALILIN SOAbu dayane yake yawan tsayamasa a rai Bashir a kullum a kowanne lkc sai yatunashi haryaji kwalla dayaga abin ...
09/12/2022

ADALILIN SO
Abu dayane yake yawan tsayamasa a rai Bashir a kullum a kowanne lkc sai yatunashi haryaji kwalla dayaga abin zainemi daga masa hankali saiya shiga addu'ar Allah yarage masa tunanin yaron yamanna son Ahmadi ajikinsa sosai har kwana sukeyi tare A karshe dai Ahmadi ne yadawo madadin bashir.
Anshafe shekara cif da dawowar Bashar gada Abuja amma ba lbrin Aure Abokansa sun dameshi sosai har zolayarsa sukeyi waiyazama tuzuru wata rana Dada takirashi tanuna masa zunzurutun bacin ranta akan rashin aurensa "Haba Bashar yanzu a ganinka mutuncinka kenan ka shafe shekaru Ashirin da bakwai da haihuwa ba Aure? duk ciki da wajen wuro yanka nasan ba mai shekarunka da za'a sameshi gwauro"fada tayi sosai har a karshe tace tasan da mahaifansa ko Baba Manu nada rai ai bai isa yakai tdawon wannan lkcin baiyi aureba duk tsarar rakinsa daga masu ya'ya uku sai mai hudu dayawama sunfara kara aure,wannan furucine yatada hankalin Bashar ya shiga fafutukar neman yarinyar dazata dace da rayuearsa ba'ajimaba ba kuwa Allah yahadashi da fadimatu wata yar fulani bazata wuce shekaru goma sha huduba tana zaune a wata rugar fulanin rugane har garasu Bashar sunayin Hausar su tar tar duk da dai sun iya sun iya filanci sosai don dashi iyayensu s**a tashi sam iyayensu basa musu hausa amma fadimatu ko hausarma tsinta takeyi bazata iyamaka kalmomi dazasu wuce hudu bataredata juya zuwa harshen fillanciba.Ba 6ata lkc aka sha hidimar bikin Bashar da fadimatu kasncewar suna son juna Bashar yayi sa'ar mata don fadimatu yarinyar kirkice duk da karancin shekarunta amma tasna yak**ata gatada ladabi da biyayya sannan ga uban kunya a kullum fuskarta a rufe take bata fiye sakewa da mutane sosaiba gara gara haulatu matar inuwa wanda ya'yanta ke kira Nenne wanda alkcin danta na uku shekararsa daya da wata hudu.fadimatu ta shafe ahekara biyar bata samu haihuwaba wanda a lkcin har Nenne ta kara haihuwa da namiji amma baizo da raiba.Allah yabawa fadimatu ciki da Nenne infa dukansu s**a haifi ya'ya mata.CIGABA

08/12/2022

ADALILIN SO.
Haka rayuwata kasance wa bashar a kauyen wuro yanka yafi samun kwanciyar hankali Acan duk da cewa akwai chanjin yanayi zaman maraya dana kaekara amma yadaure.farkon abinda yafarayi shine gyaran gidan gadonsu'gidan yadawo tsaf daga nan yafara gyara gona wanda an mamaye rabin gonar amma dai haka zai lallaba yarika bin inuwa yana ganin yadda sana'artasu take kafin yafara,kowace laraba s**anje Ngurore cin kasuwa s**ai hatsi sayarwa,abudayane yake yawan tsayamasa a rai shine bashir a kulluma

26/11/2022

SOYAYYA GAMON JINI 2

HIKAYAR ALISHARU DA YARINYA ZUMURRAZI

Da shigarsa kasuwa sai ya hangi mutane sun yi dafifi, sun zagaye wani abu a tsakiyarsu suna kallo. Sai ya ce a cikin ransa, "Shin me waÉ—annan mutane ke kallo ne, bari in matsa in É—ebe kwarkwatar ido.

Ya kutsa cikin mutane har ya kai ga abin da ake kallo. Sai ya ga ashe wata kyakkyawar kuyanga ce ake talla. Tsawon wannan kuyanga zai kai kafa biyar, jikinta madaidaici, ita ba siririya ba kuma ba mai ƙiba ba. Tana da jajayen kumatu k**ar furen wardi. Ƙirjinta faffaɗa a cike, ya turo sama k**ar zai fasa rigar da ta sanya. Tana da shafaffen ciki da faffaɗan kuturi. Wannan kuyanga ta zarce dukkanin matan zamaninta da kyawo, da haiba da kwarjini. Sunanta Zumurrazi.

Yayin da Alisharu ya ga wannan kuyanga sai ya yi mamaki da irin kyawun da Allah ya h**e mata, ya ce, "Na rantse da Allah, ba zan bar wannan wuri ba sai na ji tamanin wannan kuyanga, kuma sai na ga wanda Allah zai ba sa'ar sayenta." Don haka sai ya yi tsaye a cikin attajirai, su kuma da s**a ga haka sai s**a yi zaton cewa shi ma ya zo ne domin sayen wannan kuyanga, saboda sun san mahaifinsa ya bar masa gadon dukiya mai yawa, ba su san cewa fanko ne ba. Ganin kitse suke yi wa rogo.

Daga nan sai dillalin kuyanga ya tsaya kusa gare ta, ya dubi attajirai ya ce, "Ya ku attajirai, ya ku manyan mutane. Wanene daga cikinku zai fara taya wannan kuyanga mai daraja, sarauniyar watanni, murjanin zamani, kwararrar masaƙiya, farin cikin wanda ya same ta, baƙin cikin wanda ya rasa ta, kuyanga Zumurrazi? Duk wanda zai fara taya ta ya sani, babu komawa baya bisa ga kuɗin da ya ambata."

Daga nan sai wani tajiri ya yi gaba ya ce, "Na saye ta dinari É—ari biyar."

Sai wani ya zaburo ya ce, "Zan biya dinari É—ari biyar da goma."

Yana rufe bakinsa sai wani tsoho mai shuÉ—in idanu da matsattsar fuska, k**ar an matse lemu, mai suna Rashiduddini ya ce, "Ni zan biya dinari É—ari shida."

Sai wani ya cafe, "Zan biya dinari É—ari shida da goma."

Rashiduddini ya ce, "Na saya d

ADALILIN SO.Ya sauke gwaueon lumfashi yace"Inuwa nagode da wayannan shawarwari naka Allah yabarmu tare"dai a lkcin yatun...
22/11/2022

ADALILIN SO.
Ya sauke gwaueon lumfashi yace"Inuwa nagode da wayannan shawarwari naka Allah yabarmu tare"dai a lkcin yatuno sakon mami zainab data aiko idi direba yakawo masa wanda ko budewa baiyiba yatura cikin aljihun jakarsa ,yamike ya zuge zif din jakarsa ya fiddo leda yabude ga mamakinsa zunzurutun kudine dami dami wanda baisan iyakacin yawansuba.
Inuwane yabashi shawarar yadebi kudin ya gyara gidansu da gona su cigaba da sana'arsu tagado wato noma da sayar da hatsi sauran yayi aure dasu. yavdan kara kallon bashar yacr"ammafa mutumin ina ganin da kyar ne idan zaka iya noma yanzu ganin yadda kadade baka riki fartanyaba,subi hannunkafa lugwi lugwai tamkar nadan jajiji ,"bashar yyi dariya ,"yace inuwa bari kagai sai infika kwazo da kokari kaidai Allah yasamana albarka a cikin sana 'artamu "inuw yace Amin.
Haka rayua

Address

Kano

Telephone

+2348031800021

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SO HANA GANIN LAIFI. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to SO HANA GANIN LAIFI.:

Share