Katsina Media TV

Katsina Media TV To promote love and respect for everyone's and stand for peace and unity.

A ranar Asabar, 5 ga Satumba 2026, Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dr. Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya ƙaddamar d...
06/09/2026

A ranar Asabar, 5 ga Satumba 2026, Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dr. Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya ƙaddamar da shuwagabannin Door to Door Movement na ƙananan hukumomi 34 na Jihar Katsina.

A Karamar Hukumar Bakori, Hon. Ibrahim Dan-Alkali ne zai jagoranci shirin.

Bayan kammala taron, Dan Alkalee Masari ya naɗa Ward Coordinators guda 11 Na Karamar Hukumar Bakori domin ƙarfafa tsarin ƙungiyar daga tushe da bunƙasa hulɗa da al’umma.

Muna taya waɗanda aka naɗa murna, tare da fatan za su sauke nauyin da aka ɗora musu cikin gaskiya, ƙwazo da kishin al’umma.

Allah Ya ba mu nasara, Ya sa mu wanye lafiya. Amiin.

Sun, 6th Sep, 2026.

Yan jihar Zamfara sun gudanar da tattakin murna da jin dadi, bisa yadda shugaban kasa Tinubu ya naɗa ɗan jihar Sen Abd a...
02/09/2026

Yan jihar Zamfara sun gudanar da tattakin murna da jin dadi, bisa yadda shugaban kasa Tinubu ya naɗa ɗan jihar Sen Abd al-Aziz Yari a matsayin DG na kamfen dinsa

Iran ta yi luguden makamai masu linzami da rokoki a sansanonin sojin Amurka da ke wasu kasashen yankin Gulf, bayan da Am...
02/09/2026

Iran ta yi luguden makamai masu linzami da rokoki a sansanonin sojin Amurka da ke wasu kasashen yankin Gulf, bayan da Amurka ta sake kai mata sabbin hare-hare a cikin daren Talata wayewar Laraba.

Yau yan Kano sun gudanar da bikin Maulidin TakutahaYadda dandazon al'ummar Musulmi, mabiya Darikar Qadiriyya s**a fito z...
01/09/2026

Yau yan Kano sun gudanar da bikin Maulidin Takutaha

Yadda dandazon al'ummar Musulmi, mabiya Darikar Qadiriyya s**a fito zagayen ranar Takutuha a yau Talata, a garin Kano.

Gwamna Radda Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Kabir Faskari (KEBRAM)Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru ...
01/09/2026

Gwamna Radda Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Kabir Faskari (KEBRAM)

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi Alhaji Kabir Faskari, wanda aka fi sani da Kebram, wanda ya rasu a ƙasar Turkiyya kwanaki biyu da s**a gabata.

Marigayin Alhaji Kabir Faskari fitaccen ɗan kasuwa ne kuma sanannen ɗan asalin Jihar Katsina, wanda ya shahara wajen harkokin kasuwanci da mu’amala da al’umma.

A yayin ziyarar, Gwamna Radda ya jajanta wa iyalan marigayin, tare da addu’ar Allah Ya gafarta masa, Ya jikansa, Ya kuma ba iyalansa da yan uwansa haƙurin jure wannan babban rashi.

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, ya yi alkawarin cewa idan ya z...
01/09/2026

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, ya yi alkawarin cewa idan ya zama shugaban ƙasa, gwamnatinsa za ta tabbatar da kai kuɗaɗen da aka ware wa ƙananan hukumomi kai tsaye zuwa gare su.

Atiku ya bayyana hakan a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Kenneth Okonkwo, ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce gwamnatinsa za ta mutunta doka da oda, tare da tabbatar da ’yancin cin gashin kai na dukkan matakan gwamnati, ciki har da ƙananan hukumomi.

Ya kuma yi nuni da hukuncin Kotun Ƙoli na watan Yulin 2024 kan ’yancin cin gashin kan kuɗaɗen ƙananan hukumomi, inda ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da gazawar aiwatar da hukuncin.

Atiku ya ce gwamnatinsa za ta mutunta hukuncin kotuna, ta kare ’yancin ƙananan hukumomi, tare da tabbatar da cewa kuɗaɗen gwamnati sun isa ga al’ummar da aka ware musu.

Yadda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya isa wurin taron musamman na 21, na Tarayyar Afirka (AU), a bi...
31/08/2026

Yadda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya isa wurin taron musamman na 21, na Tarayyar Afirka (AU), a birnin Luanda, Ƙasar Angola, domin wakiltar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a taron.

Shettima ya gabatar da matsayin Najeriya a taron musamman na 21 na Tarayyar Afirka (AU) kan hare-haren kyamar baki da ƙiyayyar ’yan Afirka da ake samu a Afirka ta Kudu.

Bayan jin ƙarar harbe-harbe a Nijar: Sabbin Jiragen yaƙi da na jigilar sojoji sun sauka  birnin Niamey, babban birnin Ja...
30/08/2026

Bayan jin ƙarar harbe-harbe a Nijar: Sabbin Jiragen yaƙi da na jigilar sojoji sun sauka birnin Niamey, babban birnin Jamhuriyar Nijar, a wani fage na ƙara tsaurara tsaro da Haɗin gwiwar soji tsakanin Nijar da Aljeriya.

A yau Lahadi, jiragen yaƙi huɗu (4) kirar Sukhoi SU-30, tare da jirgin jigilar sojoji Iliouchine IL-76 da kuma jirgin dakon mai na soji Iliouchine IL-78, sun sauka a Filin Jirgin Sama na Diori Hamani da ke Niamey.

Wannan mataki na daga cikin nuna goyon bayan dabarun soji da Rundunar Sojin Aljeriya ke bai wa Rundunar Sojin Nijar.

Wannan na zuwa bayan jin ƙarar harbe-harbe a filin jirgin sama na ƙasar, a cikin daren ranar 29 ga watan Agusta 2026.

📷: CNSP

Shugaba Tinubu zai Shilla ƙasashen waje, domin hutun makwanni ukuShugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, zai bar Abu...
30/08/2026

Shugaba Tinubu zai Shilla ƙasashen waje, domin hutun makwanni uku

Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, zai bar Abuja a yau Lahadi, 30 ga Agusta 2026, domin fara hutun makonni uku na shekara-shekara.

A cewar sanarwar Fadar Shugaban Ƙasa, zangon farko na tafiyar Shugaban Ƙasar shi ne London, Birtaniya, inda zai yi hutun aiki.

Ana sa ran Shugaba Tinubu zai dawo Najeriya bayan kammala hutun, domin ci gaba da ayyukan gwamnati da kuma shirye-shiryen tunkarar zaɓen Janairu 2027.

Sanarwar ta fito ne daga Bayo Onanuga, Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabarun Sadarwa, a ranar 30 ga Agusta 2026.

INNALILLAHI WA’INNA ILAIHI RAJI’UN: Tsohon Shugaban AFAN, Arc. Kabir Ibrahim Faskari Ya RasuAllah Ya yi wa shahararren ɗ...
29/08/2026

INNALILLAHI WA’INNA ILAIHI RAJI’UN: Tsohon Shugaban AFAN, Arc. Kabir Ibrahim Faskari Ya Rasu

Allah Ya yi wa shahararren ɗan kasuwa a Jihar Katsina, kuma tsohon Shugaban Ƙungiyar Manoma ta Ƙasa (AFAN), Arc. Kabir Ibrahim Faskari, wanda aka fi sani da Kebram, rasuwa.

Kamar yadda rahotanni Ke cewa ya rasu ne a ƙasar Turkiyya a yammacin yau, Asabar.

Marigayin shi ne mamallakin babbar Kebram Plaza da ke bakin WTC a cikin birnin Katsina, inda kuma aka taɓa amfani da wani ɓangare na wajen a matsayin wurin zama na wucin gadi na Vision.

Allah Ya jiƙansa da rahama, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya sa Aljannatul Firdausi ce makomarsa.
Amin Ya Rabbal Alamin.

Address

Faskari
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Media TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share