20/08/2026
Shugaba Tinubu Ya Baiwa Kowane Ɗalibi Damar Karatu, Ya Kamata Ɗalibai Su Maida Biki — Gwamna Radda
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa tsarin rancen karatu na NELFUND da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samar, ya baiwa kowane ɗalibi damar zuwa makaranta ba tare da la’akari da halin tattalin arzikinsa ba.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya gana da ƙungiyar ɗalibai ta ƙasa reshen arewa maso yamma "National Association of Nigerian Students (NANS), Zone A", waɗanda s**a gudanar da tattaki domin nuna goyon bayansu ga Shugaba Tinubu da Gwamna Radda a zaɓen 2027.
Sakataren ƙungiyar wanda yake wakiltar shiyyar Arewa maso Yamma , Kwamared Lawal Isa Federal, ya bayyana cewa irin ci gaban da Gwamna Radda ya kawo a fannin ilimi ne ya sa ɗaliban s**a amince da sake ba shi dama, musamman biyan tallafin karatu, samar da guraben karatu a ƙasashen waje, kafa makarantu na musamman, ginawa da gyaran makarantun firamare da sakandare.
Gwamna Radda ya ce ya kamata ɗalibai su maida irin wannan ci gaba abin murna, musamman tsarin da shugaban ƙasa Asiwaju Bola Tinubu ya kawo na NELFUND, wanda ya baiwa ɗalibai damar samun ilimi ko da ba su da isasshen ƙarfin kuɗi.
Taron ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Mai Taimakawa Gwamnan Jihar Katsina kan Harkokin Ɗalibai, Hon. Muhammad Nagaske.
MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government
August 20, 2026.