Building Your Future Ambassadors

Building Your Future Ambassadors Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Building Your Future Ambassadors, Political organisation, Katsina.

SANARWA TA MUSAMMAN/RAHOTO NA TAROƘungiyar Dikko Vision Movement ta Sauya Suna zuwa“Building Your Future Ambassadors (BY...
07/05/2026

SANARWA TA MUSAMMAN/RAHOTO NA TARO

Ƙungiyar Dikko Vision Movement ta Sauya Suna zuwa
“Building Your Future Ambassadors (BYF Ambassadors)” – Jakadun Gina Makomarka

A wani muhimmin zama na Majalisar Ƙoli da ya gudana a yammacin jiya Laraba, 6 ga Mayu, 2026, ƙarƙashin jagorancin Darakta Janar, Honourable Isah Rabe Kambarawa, tare da halartar daraktocin jiha da kuma ko’odinetocin shiyyoyi, an amince da sauya sunan ƙungiyar Dikko Vision Movement zuwa “Building Your Future Ambassadors (BYF Ambassadors)”, wato Jakadun Gina Makomarka.

Da yake gabatar da jawabi a wajen taron, Darakta Janar ya bayyana cewa wannan sauyi ya zo ne a daidai lokacin da ƙungiyar ta cika shekara guda da kafuwa a shekarar 2025. Ya jaddada cewa, wannan lokaci ya dace da ɗaga tutar manufar Gwamnati kai tsaye domin ƙara bayyana ta ga al’umma baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa, a baya ƙungiyar ta kasance tana tafiya ne da sunan hangen nesa (vision) na Gwamna, amma yanzu bayan cikar shekara ɗaya, lokaci ya yi da za a fito da sunan manufar cigaban Gwamnati – “Building Your Future Strategic Policy (BYFSP)” a sarari domin ƙara bunƙasa ta da kuma yaɗa ta a tsakanin jama’a.

Darakta Janar ya lissafa manyan nasarorin da ƙungiyar ta samu a cikin wannan shekara guda, ciki har da:

Fitar da Mujallar “Gina Makomarka (MGM)”, wadda ya zuwa yanzu ta kai kusan bugu 40, tana wayar da kan jama’a kan manufofi da ayyukan Gwamnati.

Kafa tashar talabijin ta zamani – “Gina Makomarka TV”, domin isar da sahihan bayanai da shirye-shiryen wayar da kai.

Ƙirƙirar shirye-shirye masu faɗi da s**a shafi; ilimi (Education), tsaro (Security), fasahar zamani (Information Technology), lamuran mata (Women Affairs), ayyukan jin ƙai (Humanitarian Affairs), sannan sai zaɓe da harkokin siyasa (Election & Politics)

Ya bayyana cewa duk waɗannan tsare-tsare suna a matsayin ginshiƙai na tallafawa da ƙarfafa aiwatar da Tsarin Manufar “Gina Makomarka (BYFSP)”, wanda shi ne jigon gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Mai girma Gwamna Dr. Dikko Umaru Radda, CON, wanda ya bayyana a matsayin “Architect” na wannan manufa.

Taron ya jaddada cewa sabon sunan ƙungiyar zai ƙara taimakawa wajen, faɗaɗa wayar da kan al’umma kan manufofin gwamnati, haɓaka goyon bayan jama’a ga ayyukan cigaba, da gina kyakkyawar fahimta da haɗin kai tsakanin gwamnati da al’umma.

Haka kuma, an nuna cewa wannan sabon tsari zai taka muhimmiyar rawa wajen tunkarar zaɓen 2027, domin tabbatar da nasarar Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, da Shugaban Ƙasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, GCFR, in Allah Ya kaimu.

Daga cikin manyan waɗanda s**a halarci taron akwai; Honourable Muttaqa Garba Ɗangamau – Ko’odinetan Shiyyar Daura da takwaransa Honourable Mubarak Saleh Bakiyawa – Ko’odinetan Shiyyar Katsina.

Sai kuma daraktocin jiha; Honourable Sadiq Abdullahi Gwarjo – Mulki, Honourable Binta Isah – Lamuran Mata, Honourable Sama’ila Shu’aibu Marke – Matasa, da Honourable Shafi'u Ibrahim - Ayyuka da Shirye-shirye.

A ƙarshe, taron ya amince da cewa sauyin suna zuwa “BYF Ambassadors” wata babbar alama ce ta sabon babi a tafiyar ƙungiyar—wanda zai ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa, yaɗa manufofin cigaba, da kuma tabbatar da cewa saƙon “Gina Makomarka” ya isa ga kowane ɓangare na al’umma.

Sanarwa:
Daraktan Yaɗa Labarai da Sadarwa
Building Your Future Ambassadors (BYFA)
Alhamis, 7 ga Mayu, 2026
20 ga Dhul-Qa'adah, 1447

Alh. Ibrahim Kabir Masari
Aminu Bello Masari
Hannatu Musa Musawa
Katsina State Government
Renewed Hope Katsina State
City Boy Movement Katsina State

05/05/2026

MGM @36

Mujallar Gina Makomarka [MGM]:Fitowa: Talatin da Shida [36]Adadin Shafuka: 60Wannan Mujalla na ƙunshe da muhimman batutu...
05/05/2026

Mujallar Gina Makomarka [MGM]:
Fitowa: Talatin da Shida [36]
Adadin Shafuka: 60

Wannan Mujalla na ƙunshe da muhimman batutuwa game da Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Dr. Dikko Umaru Radda, CON, da aka aiwatar a makon da ya gabata, daga Litinin, 27 ga Afrilu zuwa Lahadi, 3 ga Mayu, 2026 wanda ya haɗa da:-
1. Fasahar Zamani (Information Technology)
2. Tarihi da al'ada (History & Culture)
3. Tsaro (Security)
4. Siyasa (Politics)
5. Aikin Gwamnati & Sabunta Tsarin Gudanarwa (Public Service & Administration Reform)
6. Manyan Ayyuka (Projects)
7. Tallafi (Empowerment)
8. Lamuran Sarauta (Chieftaincy Affairs)
9. Saƙonnin taya Murna (congratulatory messages)
10. Saƙonnin Jajantawa (Sympathy Messages)

Duka wannan na matsayin sakamakon yanda ake aiwatar da Tsarin Manufar Cigaba na Gina Makomarka (Building Your Future Strategic Policy BYFSP) wanda shi ne ruhin Gwamnatin Jihar Katsina ta Mai girma Malam Dikko Umaru Raɗɗa, PhD, CON.

Sanarwa:
Daraktan Yaɗa Labarai da Sadarwa
Dikko Vision Movement [DVM]
Talata, 5 ga Mayu, 2026
17 ga Dhul-Qa'adah, 1447

Katsina State Government
Renewed Hope Katsina State
City Boy Movement Katsina State

SAƘON TAYA MURNADikko Vision Movement na miƙa saƙon taya murna na musamman ga Injiniya Dr. Muttaqa Rabe Darma bisa nadin...
23/04/2026

SAƘON TAYA MURNA

Dikko Vision Movement na miƙa saƙon taya murna na musamman ga Injiniya Dr. Muttaqa Rabe Darma bisa nadinsa da aka yi a matsayin Ministan Samar da Gidaje da Cigaban Birane na Tarayyar Najeriya.

Wannan babban matsayi da Shugaban Kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, GCFR ya ba shi ya zo ne a daidai lokacin da ƙasa ke buƙatar ƙwararru masu hangen nesa, nagarta da kuma kwarewa a fannin shugabanci. Injiniya Dr. Muttaqa Rabe Darma ya kasance gogaggen ɗan siyasa kuma jajirtaccen mai mulki, wanda tun bayan kammala aikinsa a matsayin Shugaban PTDF, bai gushe ba yana tare da al’ummarsa, yana sauraron buƙatunsu tare da tallafa musu ta hanyoyi daban-daban.

Hakazalika, ya kasance attajiri mai zuciyar bayarwa, wanda ya kafa Umaru Musa Yar’adua Capacity Centre a Jihar Katsina—wani gagarumin cibiyar da ke ba matasa da al’umma damar koyon sana’o’i, ilimi da ƙwarewa domin dogaro da kai.

Muna da cikakken yaƙini cewa, wannan sabon matsayi zai zama wata dama gare shi na ci gaba da nuna ƙwarewarsa da sadaukarwarsa wajen kawo cigaba mai ɗorewa a fannin gidaje da bunƙasa birane a faɗin ƙasar nan.

Muna addu’ar Allah Ya ba shi ikon sauke nauyin wannan amanar da aka ɗora masa cikin nasara, tare da shiryar da shi a dukkan matakan aikinsa.

Sanarwa:
Daraktan Yada Labarai da Sadarwa
Alhamis, 23 ga Afrilu, 2026
6 ga Dhul-Qa’adah, 1447

Dr. Dikko Umaru Radda
Alh. Ibrahim Kabir Masari
Aminu Bello Masari
Renewed Hope Katsina State
City Boy Movement Katsina State

Dikko Vision Movement (DVM) ta yi Alhinin Rasuwar Mai ɗakin Shugaban Ma'aikatan Fadar GwamnatiDikko Vision Movement (DVM...
14/04/2026

Dikko Vision Movement (DVM) ta yi Alhinin Rasuwar Mai ɗakin Shugaban Ma'aikatan Fadar Gwamnati

Dikko Vision Movement (DVM) na miƙa saƙon ta’aziyya mai cike da alhini da jimami bisa rasuwar Hajiya Hawwa (Maijidda) Abdulƙadir Mamman Nasir, matar Shugaban Ma’aikata (Chief of Staff) na Fadar Gwamnatin Jihar Katsina.

Lallai wannan rashi babbar asara ce ba ga mijinta da iyalanta kaɗai ba, har ma da al’umma baki ɗaya, duba da irin gudunmawar da ta bayar wajen tarbiyya, tausayi da kuma kyautata zamantakewa. Mutuwa gaskiya ce, kuma kowa zai ɗanɗana ta a lokacin da Allah Ya ƙaddara.

DVM na jajanta wa mijinta, Shugaban Ma’aikata na Fadar Gwamnati, tare da iyalansu da sauran ‘yan’uwa, tare da addu’ar Allah Ya ba su juriya da haƙurin jure wannan babban rashi.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta mata, Ya yafe kura-kuranta, Ya sa Aljannatul Firdausi ta zama makomarta. Haka kuma, Allah Ya ƙara haɗa zukatan waɗanda ta bari a baya, Ya kuma ba su ikon ci gaba da raya kyawawan halayenta.

Za a yi jana’izarta a gobe Laraba, 15 ga Afrilu, 2026, da ƙarfe 1:00 na rana bayan sallar Zuhr a Masallacin GRA. Muna kira ga al’umma da su halarta tare da yi mata addu’ar rahama.

Allah Ya jikanta da rahama, Ya sa Aljanna ce makomarta. Amin.

Sanarwa:
Daraktan Yaɗa Labarai da Sadarwa
Dikko Vision Movement (DVM)
Talata, 14 ga Afrilu, 2026
26 ga Shawwal, 1447 AH

Dr. Dikko Umaru Radda
Alh. Ibrahim Kabir Masari
Aminu Bello Masari
Katsina State Government

Dikko Vision Movement Ta Ziyarci Ko'odinetan Renewed Hope na Jihar Katsina, Ta Jaddada Goyon Bayan Zaɓen Shugaba Tinubu ...
14/04/2026

Dikko Vision Movement Ta Ziyarci Ko'odinetan Renewed Hope na Jihar Katsina, Ta Jaddada Goyon Bayan Zaɓen Shugaba Tinubu a 2027

Dikko Vision Movement (DVM) ta kai wata muhimmiyar ziyarar girmamawa ga Ko’odinetan Jakadun Sabunta Fata (Renewed Hope Ambassadors) na Jihar Katsina, kuma tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina (1999-2003), Alhaji Tukur Ahmed Jiƙamshi, a yammacin jiya Litinin, 13 ga Afrilu, 2026, inda ta sake jaddada cikakken goyon bayanta ga nasarar Shugaban Ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027, in Allah Ya kaimu.

Tawagar tafiyar ta samu jagorancin Darakta Janar na DVM, Honourable Isah Rabe Kambarawa. A yayin ziyarar, Darakta Janar ya fara da miƙa saƙon ta’aziyya ga Ko’odinetan bisa ibtila’in harin ‘yan bindiga da ya afka wa al’ummar mahaifarsa ta Jiƙamshi, a ƙaramar hukumar Musawa, a cikin azumin Ramadan da ya gabata.

Bayan haka, ya taya shi murnar naɗin da Shugaban Ƙasa ya yi masa a matsayin jagoran shirin Jakadun Sabunta Fata na ƙasa reshen Jihar Katsina. Ya bayyana cewa wannan naɗi ya dace da ƙwarewa da gogewar da Alhaji Tukur Ahmed Jiƙamshi ke da su, musamman la’akari da irin gudunmawar da ya bayar a matsayinsa na tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina tsakanin shekarun 1999 zuwa 2003. Ya kuma yi masa fatan alheri da addu’ar samun ikon sauke nauyin da aka ɗora masa, tare da tabbatar da nasarar Shugaban Ƙasa a zaɓen 2027.
Bugu da ƙari, Darakta Janar ya yi cikakken bayani kan asalin kafa Dikko Vision Movement (DVM), manufofinta da tsare-tsarenta, inda ya bayyana cewa ƙungiyar na aiki ne domin tallafawa Tsarin Gina Makomarka (Building Your Future Strategic Policy - BYFSP). Daga cikin manyan nasarorin ƙungiyar akwai ci gaba da wallafa Mujallar Gina Makomarka (MGM) wanda zuwa yanzu an fitar da Mujallar sau 35, da kuma kafuwar tashar Gina Makomarka TV, waɗanda ke taimakawa wajen yaɗa manufofin gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Katsina Dr. Dikko Umaru Radda, CON.

Haka zalika, ya bayyana shirye-shiryen (initiatives) da ƙungiyar ke da su na gaba, waɗanda aka tsara domin ƙarfafa manufar gwamnatin jihar da inganta walwalar al’umma.

A nasa ɓangaren, Ko’odinetan Jakadun Sabunta Fata na Jihar Katsina, Renewed Hope Katsina State, Mai Girma Alhaji Tukur Ahmed Jiƙamshi, ya yaba da tsari da hangen nesa na Dikko Vision Movement, yana mai cewa an gina ta ne bisa manufa mai ɗorewa da za ta taimaka wajen ciyar da harkokin siyasa da ci gaban al’umma gaba.

Ya kuma tabbatar da aniyar sa ta yin aiki kafaɗa-da-kafaɗa da ƙungiyar domin tabbatar da nasarar gwamnatin Shugaban Ƙasa tare da samun nasarar zaɓensa a shekarar 2027. Bugu da ƙari, ya nuna cikakken goyon baya ga shirye-shiryen DVM, musamman waɗanda s**a shafi muhimman fannoni na ci gaba.

Daga cikin manyan waɗanda s**a halarci taron sun haɗa da Daraktan Mulki na Jiha, Honourable Sadiq Abdullahi Gwarjo; Daraktar Harkokin Mata, Honourable Binta Isah; Daraktan Matasa, Honourable Sama’ila Shu’aibu Marke; Shugaban Matasan DVM na Shiyyar Daura, Honourable Nura Abdulraqib; Shugabar Mata ta ƙaramar hukumar Dutsin-Ma, Honourable Hassana Uzairu; da kuma Ko’odinetoci da sauran mambobin DVM daga ƙananan hukumomi da mazaɓu daban-daban.

Wannan ziyara na nuni da ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin ƙungiyoyin siyasa da masu ruwa-da-tsaki domin tabbatar da ɗorewar nasarorin gwamnati da kuma shimfiɗa turbar ci gaba mai ɗorewa.

Sanarwa:
Daraktan Yaɗa Labarai da Sadarwa
Dikko Vision Movement - DVM
Talata, 14 ga Afrilu, 2026
26 ga Shawwal, 1447


Alh. Ibrahim Kabir Masari
Aminu Bello Masari
City Boy Movement Katsina State
Prof Nentawe Yilwatda
Katsina State Government
Ibrahima Kaulaha Mohammed

13/04/2026

Mujallar Gina Makomarka (MGM) @ 35
Dr. Dikko Umaru Radda

Mujallar Gina Makomarka [MGM]:Fitowa: Talatin da Biyar [35]Adadin Shafuka: 28Wannan Mujalla na ƙunshe da muhimman batutu...
13/04/2026

Mujallar Gina Makomarka [MGM]:
Fitowa: Talatin da Biyar [35]
Adadin Shafuka: 28

Wannan Mujalla na ƙunshe da muhimman batutuwa game da Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umaru Raɗɗa, PhD, CON, da aka aiwatar a makon da ya gabata, daga Litinin, 6 zuwa Lahadi, 12 ga Afrilu, 2026 wanda ya haɗa da:-
1. Tattalin arziƙi (economy)
2. Wutar Lantarki da Makamashi (power and energy)
3. Cigaban al'umma (community development)
4. Ilimi (education)
5. Saƙonnin taya murna (congratulatory messages)

Duka wannan na matsayin sakamakon yanda ake aiwatar da Tsarin Manufar Cigaba na Gina Makomarka (Building Your Future Strategic Policy BYFSP) wanda shi ne ruhin Gwamnatin Jihar Katsina ta Malam Dikko Umaru Raɗɗa, PhD, CON.

Sanarwa:
Daraktan Yaɗa Labarai da Sadarwa
Dikko Vision Movement [DVM]
Litinin, 13 ga Afrilu, 2026
25 ga Shawwal, 1447

Dr. Dikko Umaru Radda
Alh. Ibrahim Kabir Masari
Aminu Bello Masari
Renewed Hope Katsina State
City Boy Movement Katsina State

Ya Allah muna roƙonka da sunayenka Al-Hayyu Al-Qayyum da kada ka gajiyar da wannan bawa naka Dr. Dikko Umaru Radda, a ƙo...
06/04/2026

Ya Allah muna roƙonka da sunayenka Al-Hayyu Al-Qayyum da kada ka gajiyar da wannan bawa naka Dr. Dikko Umaru Radda, a ƙoƙarinshi na ganin cewa, an samu zaman lafiya, a ko'ina a faɗin Jihar Katsina.

Ya Ubangiji Al-Ƙahharu ka iya mashi abin da ba ya iyawa, ka ƙara riƙo da hannuwanshi domin ganin bayan wannan jarabawa baki ɗaya, da sauran jarabawowi, a wannan Jiha tamu mai albarka.

Amin Ya Hayyu Ya Qayyum

06/04/2026

Mujallar Gina Makomarka (MGM) @ 34
Dr. Dikko Umaru Radda

Address

Katsina
820

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Building Your Future Ambassadors posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share