Faruk Sule Garo 4rum

Faruk Sule Garo 4rum Ni mutum ne kamar kowa,kuma maison cigaban al'umarsa,musamma mutanen Gwarzo da Kabo

20/07/2023
We would like to use this opportunity to inform all our teeming supporters and well-wishers about developments with rega...
31/05/2022

We would like to use this opportunity to inform all our teeming supporters and well-wishers about developments with regards to the APC House of Representatives primary elections. On Friday, the 27th of May, we had a long meeting and held discussions with our party representatives and regional stakeholders till about 3pm at Africa House, Kano State Government House. The party leadership decided that they will zone the House of Representatives position to Gwarzo rather than Kabo LGA because the past 16 years has seen leadership from Kabo LGA. In addition, the Deputy Governorship position in Kano State has been zoned to Kabo, by consensus.

This came as a great disappointment to Hon. Dr. Farouq Sule Garo as he was primed and ready for the primary elections and would have very much preferred for the democratic rule of law to take precedence.

Right from time, Hon. Dr. Farouq Sule Garo’s ambition in politics has been to seek office for the betterment of his people, region and state. It goes without saying that he will continue to do this regardless of whether he holds a political office or not.

We are therefore using this opportunity to sympathise with the people of Kabo and Gwarzo on such a missed opportunity, to be represented by one of its finest sons, and to bring the much needed development to the constituency. Nevertheless, we put our faith in Allah SWT to grant victory to whom He pleases and when He pleases. We therefore pray that He chooses for us what is best.

Yours sincerely,

Yahaya Umar Masanawa
Hon. Dr. FAROUQ SULE GARO Spokesperson

JINJINA ZUWA GA MATASA MASU AMFANI DA KAFAR SADARWA TA ZAMANI AKAN IRIN MUHIMMIYAR RAWAR DA KUKE TAKAWA WAJEN KARE MURAD...
15/10/2021

JINJINA ZUWA GA MATASA MASU AMFANI DA KAFAR SADARWA TA ZAMANI AKAN IRIN MUHIMMIYAR RAWAR DA KUKE TAKAWA WAJEN KARE MURADAN HONORABUL FAROUK SULE GARO

Daga: Comrd Yahaya Umar Kabo

Hakika Jajirtattun Matasanmu masu amfani da Kafar Sadarwa ta Zamani a Jihar Kano (Social Media) musamman yankinmu na Gwarzo da Kabo dama sauran sassan jiha, kuna taka muhimmiyar rawa a fagen Siyasar Honorabul Farouk Sule Garo wajen kare Qima da mutuncin sa dakuke yi.

Haka zalika hazikkan Matasan mu suna cigaba da taka rawa ba dare ba rana, a kowane lokaci domin dada bayyana manufofin Honorabul Farouk Sule Garo tareda karfawawa al'umma gwiwa wajen ganin zabe mai zuwa na shekara 2023 basu kara bari anyi masu sakiyar da babu ruwa a cikin taba.

Domin Idan mukayi la'akari da ire-iren Gwagwarmayoyin da Matasan mu, s**a sha musamman Manya da Kananan magoya bayan Hon-FSG suke fuskantar kalubale da dama a zabukan dasu ka gabata, zamu ga yadda aka gudanarda chakwakiyar wata irin Siyasa a shekarar 2019, domin anyi walkiya munga kowa, kana kuma mun san gidan su kowa don haka dole ne mukara yaba maku ga irin kokarin da wadannan jajirtattun Matasan s**ayi.

Domin kuwa wadannan hazikan Matasan sun jure duk wani zagi da muzgunawa ga jama'a tareda furta musu miyagun kalamai da barazana ga rayuwarsu duk wajen kare Qima da mutuncin Honorabul Farouk Sule Garo da kuma muradan sa.

Daga karshe Ina rokon Allah SWT ya taimaki mai girma Honorabul Farouk Sule Garo ya bashi mulkin Gwarzo da Kabo a zabe mai zuwa na 2023, sannan Allah ya kara taimakon Matasanmu masu amfani da Kafar Sadarwa ta Zamani (Social Media) ya basu ikon cigaba da hakuri yasa suci gajiyar wahalhalun da s**ayi da romon dimukradiyya.

✍🏻signed: Garkuwan-FSG dan mutan

TSARABAR JUMA'A...Allah duk alkhairin da ke tattare da wannan ranar mai tarin albarka, Allah ka kawo manashi, Akasin hak...
15/10/2021

TSARABAR JUMA'A...

Allah duk alkhairin da ke tattare da wannan ranar mai tarin albarka, Allah ka kawo manashi, Akasin hakan kuma ka kare mu dashi. Amin👏🏻👏🏻👏🏻

Yaa Allah 'Yan uwan mu dake cikin ko wane qangi da masifa na rayuwa, Allah ka kawo masu sauqin shi, Wadanda s**a rigamu zuwa gidan gaskiya Allah ka yi masu rahama. Amin👏🏻👏🏻👏🏻

Allah mutanen mu dake jihohin Sokoto, da kuma na Zamfara, Katsina, Niger, da kuma Kaduna, kafimu sanin tashin hankalin da suke ciki Allah kayi musu maganin shi, mu kuma ka qara tsare mu, ka yalwantar da zaman lafiya a qasarmu baki daya. Amin👏🏻👏🏻👏🏻

Allah duk wanda yake a hannun masu garkuwa da mutane, Allah ka kubutar dashi cikin lafiya da aminci, Masu yi kuma idan har suna da niyyar bari Allah ka basu ikon tuba. Amin👏🏻👏🏻👏🏻

Allah duk buqatocin mu na alkhairi ka fimu saninsu, Allah ka cika mana su domin kai ne Kareemun kuma Raheemun. Amin ya Allah👏🏻👏🏻👏🏻

daga tsangayar masoya mai girma Babban Mataimaki na musamman ga Mai Girma Gwamna akan kimantawa da saka idanu akan dukkanin ayyuka da al’amuran Gwamnatin Jihar Kano, Honorabul Farouk Sule Garo.

2023: GWARZO DA KABO CANCANTA ZAMU ZABADaga: Ashiru Ibrahim KaboKowa Yafito Muhada Karfi Da Karfe Domin Mukai Maison Cig...
11/10/2021

2023: GWARZO DA KABO CANCANTA ZAMU ZABA

Daga: Ashiru Ibrahim Kabo

Kowa Yafito Muhada Karfi Da Karfe Domin Mukai Maison Cigabanmu, Wakilcinmu A Majalisar Tarayyar Najeria (Abuja) Wanda Yasan Inda Yake Mana Kaikayi Wanda Yake Iya Samawa Matasanmu Ayyukan Yi, Wanda Yake Gina Rayuwar Alummarmu , Wanda Yasan Ciwonmu , Mai Kishin Mata Da Matasa Da Dattijanmu,
Mai Girma Haziki Kuma Jajirtaccen Babban Mataimaki na musamman ga Mai Girma Gwamna akan kimantawa da saka idanu akan dukkanin ayyuka da al’amuran Gwamnatin Jihar Kano

Sannan Muna Kira Ga Al'ummar Gwarzo Da Kabo Akan Muyi Tururuwa da fitar dango wajen zaben Honorabul Farouk Sule Garo, wajen ganin mai girma Babban Mataimaki na musamman ga Mai Girma Gwamna akan kimantawa da saka idanu akan dukkanin ayyuka da al’amuran Gwamnatin Jihar Kano Hon-FSG ya Wakilce mu A Kakar Zabe Ta 2023 Domin Samun Kyakyawan Wakilci Wanda Za muyi Alfahari Dashi .

Da Fatan Ubangiji Allah Ya Tabbatar Da Mai Girma Babban Mataimaki na musamman ga Mai Girma Gwamna akan kimantawa da saka idanu akan dukkanin ayyuka da al’amuran Gwamnatin Jihar Kano Honorabul Farouk Sule Garo A Matsayin Zababben Dan Majalisar Tarayyar Najeria Mai Wakiltar Kananan Hukumominmu Na Gwarzo da Kabo Masu Albarka Ameen Summa Ameen

_______
✍🏻signed: Garkuwan-FSG dan mutan

Sakon Fatan Alheri Ga Ilahirin 'Yan Social media na-Hon FSGDaga: Honorabul Farouk Sule GaroZan yi amfani da wannan damar...
08/10/2021

Sakon Fatan Alheri Ga Ilahirin 'Yan Social media na-Hon FSG

Daga: Honorabul Farouk Sule Garo

Zan yi amfani da wannan damar inkara yabawa da jinjinawa duk wani d'an social media na gidana a bisa jajircewa da kokarin da suke nunawa ba dare ba rana na ganin tafiyar nan ta cigaba da samun magoya baya.

Kamar su:
Ashiru Ibrahim Kabo
Salim Abdu Garo
Muazu Tayyo kabo
Auwal Zubairu Kiru
Aliyu Kabiru Bari
Safullahi Dan gaske
Yahaya Masanawa
El-Nasir Balan
Comrd Najibu Idris
Abba Umar Alkadiri
Da sauran su

Sannan masu turo sakonnin fatan alheri kuma ina godiya a gareku da irin kaunar da kuke nuna min, sannan ga duk mai bukatar shiga wannan tafiya mai albarka domin ciyar da yankinmu da jiharmu da kuma kasa baki daya to kofa a bude ta ke.

Za ku iya tuntubar wannan lambar 08033055199 ta Garkuwan-FSG.

Nagode! Nagode!! Nagode!!! Masoya

DASANNU ALLAH ZAI KAIKA INDA MAKIYA BASU ZATA BA, KUMA DA KARFIN IKONSA SAI KA WAKILCI GWARZO&KABO A SHEKARA TA 2023Daga...
08/10/2021

DASANNU ALLAH ZAI KAIKA INDA MAKIYA BASU ZATA BA, KUMA DA KARFIN IKONSA SAI KA WAKILCI GWARZO&KABO A SHEKARA TA 2023

Daga: Comrd Yahaya Umar Kabo

Mai hankali yana yin tunani ako yaushe, saboda bahaushe yana cewa bakin ciki kashe mai yin ka.

Ba mu cewa sai kowa ya soka, domin duk da shugaban halitta da aka aikowa mutane da aljannu wasu basu son sa kuma kiyayya suke yi da shi balantana kai, masu hassada, da masu kiyayya ko adawa da kai saboda girma da daukakar da Allah ya baka ne, kuma wannan shine gishirin rayuwar dan adam samun mai hasadarsa ko kiyayya da shi.

Domin wasu daga cikin suma ka taimaki iyayensu sannan su kansu ka taimakesu amma basu sonka, wasu kuma arziki suke nema a wurinka basu samu ba saboda sun manta da ba kai ne kake bada arzikin ba domin arzikin kowa yana wajen Allah a saboda haka ne suke yin kiyayya da hassada da kai.

Mu akidar mu itace ayi hakuri asha yada aka dama, da dadi da ba dadi ayi hakuri domin wata rana sai labari, kuyi hakuri abokanan gwagwarmaya ku dawo mu cigaba da tafiya kamar yadda muka saba.

Domin mu dukan wata mafita ta alkhairi, da cigaban rayuwar Honorabul Farouk Sule Garo wallahi muna yi, sannan muna rokon Allah yasa girmansa ya wuce yanda yake yanzu, manufarsa ta alkhairi ga al'umma Allah ya kara nin-ninkata ga al'umma, Allah ya kara daukaka girmansa da darajarsa, duk inda kayyi muna nan bayanka da ikon Allah

✍🏻signed: Garkuwan-FSG dan mutan

SOYAYYAR GASKIYA BA'A JIN KASALA WURIN NUNATA A KOWANE YANAYI.Daga: Comrd Yahaya Umar KaboSunan wannan rubutun jirwaye m...
08/10/2021

SOYAYYAR GASKIYA BA'A JIN KASALA WURIN NUNATA A KOWANE YANAYI.

Daga: Comrd Yahaya Umar Kabo

Sunan wannan rubutun jirwaye mai kamar wanka saboda wasu 'ya'yan kuka 'ya'yan da suke jawa iyayen su jefa, amma ayi hakuri ban so inyi wannan rubutun ba, kawai dai kamawa tayi shiyasa zan yi masu raddi irin na siyasa.

Soyayyarmu Ga Honorabul Farouk Sule Garo, a Duniya Babu Wani abu da zai tunkaro mu, muji Jikinmu Yayi Sanyi, ko muji wata Kasala wajen Kare Martabar sa da Mutuncin sa da Kimarsa a wajen kowaye.

Saboda haka Magauta, Makiya, mahassada da masu sharri da kuke neman kasawar sa takowane irin hali kusani cewa Kifi na ganin ku masu jarkoma.

Domin Mun San Salon irin cin mutunci mai mutunci da kuke yi, Mun San ta inda kuke Bullowa Munsan Inda kuka Dosa a rayuwar ku, domin abin da kuke yi gado ne, sannan kusani Bazamu Taba Bari Wadannan Magautan da Makiyan Suyi Amfani da Wata Dama ba, Suna Jifansa da Sharruka Domin Wata Biyan Bukatar su.

Ya Allah Kabaiwa Wannan Bawa Naka Honorabul Farouk Sule Garo nasarori Akan Dukkanin Abunda Yassanya A gabansa akusa ko anesa.

Nan gaba kadan zan lissafo su domin mun san tarihin ku da tarihin masu....?

✍🏻signed: Garkuwan-FSG dan Mutan

RIMI KAKE ADON GARI DAN GALADIMAN GARO, FITILAR AL'UMMA BABBAN SSA.Daga: Comrd Yahaya Umar KaboIlimi na daya daga cikin ...
07/10/2021

RIMI KAKE ADON GARI DAN GALADIMAN GARO, FITILAR AL'UMMA BABBAN SSA.

Daga: Comrd Yahaya Umar Kabo

Ilimi na daya daga cikin abubuwan da kowace irin al'umma su ke da bukatar sa, musamman ma Matasan mu na wannan zamani.

Domin barin al'umma turus kara zube babu ilimi, alama ce da ta ke nuna cewa, wannan al'ummar tana zaune ne a cikin dukununu duhun jahilci, domin sai da ilimi mutum ya ke iya gane inane ya ke yimasa ciwo a rayuwa.

Ko kuma inane ya kamata ace ya saita alqibilar sa ta dosa domin taimakawa al'ummar da ya ke zaune a cikin ta, domin shi ilimi fitilace ga rayuwar dan Adam, don ko a addinin mu Na Musulunci haramun ne mutum ya zauna babu ilimi.

Shiyasa Garkuwan al'ummar Gwarzo da Kabo wato sabon babban Mataimaki na musamman ga Mai Girma Gwamna akan kimantawa da saka idanu akan dukkanin ayyuka da al’amuran Gwamnatin Jihar Kano, Honorabul Farouk Sule Garo ya dukufa wajen ganin ya samar da ingantaccen ilimi mai dorewa ga al'umma.

Domin yakar jahilci a cikin al'umma da zama babu aikin yi, adon haka nema mai girma Honorabul Farouk Sule Garo ya bude cibiyar taimakon al'umma mai suna (Farouk Sule Garo Foundation) a turance, don amfanin Matasan mu wanda idan rayuwar su tayi kyau babu shakka al'umma ta gyaru.

Sannan Matasa ku kara kwantar da hankalin ku domin mai girma babban SSA ya ce, a gayamaku akwai sabbin tsare-tsare wanda wannan cibiya zata kawo maku, domin amfanin al'umma.

✍🏻signed: Garkuwan-FSG dan mutan .

Address

Kano Kabo
Ogere

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Faruk Sule Garo 4rum posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share