14/04/2026
🛑SANARWA TA MUSAMMAN🛑
Daga
(Kwankwasiyya Movement Kano State Youth Leader)
Akan Niyyar Tsayawa Takarar Kujerar Dan Majalisar Jiha - Karamar Hukumar Rogo (2027) a karkashin jam'iyyar ADC
ASSALAMU ALAIKUM WA RAHMATULLAH,
Muna farin cikin sanar da al'ummar Karamar Hukumar Rogo, musamman mazabu goma dake cikinta, cewa Hon. Saddam Umar Fulatan ya bayyana cikakkiyar niyyarsa ta tsayawa takarar neman kujerar Dan Majalisar Jiha a zaben shekarar 2027, a karkashin jam'iyyar ADC, bisa tafiyar Kwankwasiyya
Wannan mataki ya biyo bayan tuntuba mai zurfı da aka yi da al'umma, dattawa, matasa da sauran masu ruwa da tsaki a fadin Karamar Hukumar Rogo. Ra'ayoyin al'umma da goyon bayan da ake ci gaba da samu sun karfafa wannan kuduri domin samar da wakilci na gaskiya, adalci da ci gaba.
Hon. Saddam Fulatan matashi ne jajirtacce, mai kishin al'umma, wanda ya dade yana hidima a matakai daban-daban. Tarihinsa na aiki da sadaukarwa shaida ne kan irin wakilci nagari da al'ummar Rogo za su samu idan aka ba shi dama.
Muna da yakinin cewa, a karkashin inuwar jam'iyyar ADC, tare da goyon bayan al'umma, Hon. Saddam Fulatan zai samu nasarar tsayawa takara kuma, da yardar Allah, zai samu nasara a zaben 2027.
Muna kira ga daukacin al'ummar Rogo da su kasance tare da mu a wannan tafiya ta alheri domin gina makoma mai kyau ga kowa.
Allah Ya ba mu nasara. Ameen.