24/10/2025
DAN MAJALISAR TARAYYA NA SABON GARI YA KARBI KATIN JAM’IYYAR APC A WARD DINSA
A yau Jumu’a, 24 ga Oktoba, 2025, Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Sabon Gari Federal Constituency, ya karɓi katin zama ɗan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Hanwa Ward, cikin Sabon Gari Local Government Area, Kaduna State, Nigeria.
Taron karɓar katin jam’iyyar ya samu halartar shugabannin jam’iyyar APC na matakai daban-daban, magoya baya, da manyan ‘yan siyasa daga sassa daban-daban na jihar.
A yayin karɓar katin nasa, Dan majalisar ya bayyana cewa matakin da ya ɗauka na komawa jam’iyyar APC na da nasaba da ci gaba da haɗin kai, cigaban al’umma, da kuma tabbatar da ingantaccen wakilci ga jama’ar Sabon Gari.
Ya kuma gode wa shugabannin jam’iyyar da magoya bayansa bisa irin goyon bayan da s**a nuna masa tun daga farko har zuwa wannan lokaci.
Signed By Hon Sadiq Ango Abdullahi Media Team Member House Of Representative Sabon Gari Federal Constituency, Deputy Chairman House Committee On FERMA ✍️