07/07/2026
HON. HAMZA SULAIMAN FASKARI, WAMBAN FASKARI, SADAUKIN ƘASAR HAUSA I
Rayuwar Jagora Mai Kishin Jama'a da Ci Gaban Al'umma
Daga: Saidu Almu Munhaye
07/07/2026.
A tarihin al'ummomi, akan samu mutane kaɗan waɗanda Allah ke yi wa baiwar shugabanci, hangen nesa da kuma son hidimtawa jama'a ba tare da nuna gajiyawa ba. Irin waɗannan mutane su ne ke zama fitilu masu haskaka tafarkin ci gaba, suna barin tarihi mai ɗorewa a zukatan al'umma. Daya daga cikin irin waɗannan jagorori shi ne Hon. Hamza Sulaiman Faskari, wanda aka fi sani da Wamban Faskari kuma Sadaukin Ƙasar Hausa
An haifi Hon. Hamza Sulaiman Faskari a garin Faskari da ke Jihar Katsina, cikin gida mai cike da tarbiyya, ilimi da hidimar jama'a. Mahaifinsa, marigayi Alhaji Sulen-Sule Faskari, ya yi fice a matsayin manomi, ɗan kasuwa, ɗan siyasa kuma mai taimakon al'umma, yayin da mahaifiyarsa, Hajiya Ruqayya, ta shahara da kyawawan ɗabi'u da tarbiyyar addini. Tun yana ƙarami ya fara karatun Alƙur'ani, kafin daga bisani ya shiga makarantun boko domin neman ilimin zamani.
Kishinsa ga ilimi ya sa ya samu digirin farko na Bachelor of Arts (History) daga Jami'ar Bayero Kano a shekarar 2004, sannan ya ƙara samun digirin Master of Public Policy and Administration daga wannan jami'a a shekarar 2008. Baya ga haka, ya halarci ƙarin horaswa a fannin kwamfuta da sauran shirye-shiryen ƙwarewa, yana mai tabbatar da cewa ilimi shi ne ginshiƙin ci gaba.
Bayan kammala karatu, Hon. Hamza ya fara aiki a Hukumar Federal Character Commission a shekarar 2009. Daga baya, a shekarar 2011, aka naɗa shi Mataimaki na Musamman ga Sanata Abu Ibrahim a Majalisar Dokoki ta Ƙasa. Waɗannan muk**ai sun ba shi damar ƙara fahimtar shugabanci, gudanar da mulki da kuma hidimar jama'a.
A harkokin siyasa kuwa, Hon. Hamza ya zama ɗaya daga cikin fitattun jagororin APC a Jihar Katsina. Saboda ƙwarewa, jajircewa da amana, Gwamna Aminu Bello Masari ya naɗa shi Kwamishinan Muhalli a shekarar 2015, sannan aka sake ba shi wannan amanar a wa'adi na biyu. Ya ci gaba da riƙe manyan muk**ai a gwamnatin Malam Dikko Umaru Radda, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen aiwatar da manufofin ci gaban jihar.
Sai dai abin da ya fi sa sunansa ya yi armashi shi ne ayyukan jin ƙai da yake gudanarwa. Ya taimaka wajen inganta cibiyoyin lafiya, samar da ruwan sha, tallafa wa marasa lafiya, ɗalibai, marayu, mata da matasa, tare da shirye-shiryen koyar da sana'o'i da ba da jari domin dogaro da kai. Haka kuma ya ba da gudummawa wajen kare muhalli da magance matsalolin ambaliya da zaizayar ƙasa a sassa daban-daban na Jihar Katsina.
Irin wannan sadaukarwa ce ta sa aka naɗa shi Wamban Faskari, sannan daga bisani Mai Martaba Sarkin Daura ya ba shi sarautar Sadaukin Ƙasar Hausa I, sarauta mai ɗimbin tarihi da martaba, domin girmama irin gudummawar da yake bayarwa ga al'umma da ƙasar Hausa baki ɗaya.
A yau, Hon. Hamza Sulaiman Faskari yana ci gaba da zama abin koyi ga matasa da shugabanni. Ana kallonsa a matsayin jagora mai hangen nesa, mai son haɗin kai, zaman lafiya da ci gaban al'umma. Wannan ne ya sa magoya bayansa da dama suke bayyana cewa zai iya wakiltar muradun al'ummar Kankara, Faskari da Sabuwa yadda ya k**ata a Majalisar Wakilai ta Tarayya idan aka ba shi dama. An kuma ruwaito cewa shugabannin APC a yankin sun amince da shi a matsayin ɗan takarar sulhu na mazabar gabanin zaɓen 2027.
Hon. Hamza Sulaiman Faskari ya tabbatar da cewa shugabanci ba magana ba ne kawai, aiki ne, amana ce, da sadaukarwa. Tarihinsa ya nuna cewa ci gaban al'umma yana samuwa ne idan shugaba ya fifita bukatun jama'a fiye da nasa.
"Jagora nagari shi ne wanda tarihinsa ke rayuwa a cikin zukatan al'umma saboda ayyukan alheri da ya bari."
GOBEN ZATA FI YAU DIN KYAU INSHA ALLAH.