08/11/2021
Babban Burina Shine Allah Ya Cigaba Da Bani Iko Na Zama Sanadiyar Samun Sauƙin Bayin Allah, Cewar A.A Zaura
..ƙoƙarina akan haɓaka harkar Ilimi ba ɗan ƙarami ba ne...
Babban mai taimakon al'umma kuma mai ruwa da tsaki a Jam'iyar APCn Jihar Kano kuma shugaban Gidauniyar "AA Zaura Foundation", His Excellency Abdulkarim Abdussalam Zaura ya bada tabbacin cewa, ƙoƙarinsa na haɓɓaka harkar Ilimi a faɗin jihar Kano ta amfani da gidauniyarsa ba abu ba ne da zai gajiya a kai, ganin irin muhimancin da Ilimin yake da shi ga rayuwar al'umma.
Zaura ya bayyana haka ne a yammacin ranar Asabar, yayin da yake halartar bikin yaye ɗalibai karo na 7 da 8 a Jami'ar Base dake Babban Birnin Tarayya Abuja.
Zaura wanda shima ya samu kammala karatun Digiri na biyu akan harkar gudanar da Gwamnati da Kimiyar Siyasa wato (M.sc Political Science and Public Administration) daga tsangayar Gudanarwa da Kimiyar zamantakewar ɗan Adam na Jami'ar, inda ya zamo ɗaya daga cikin zakaran gwajin dafi a wannan tsangayar wanda hakan yasa ya zama ɗaya daga cikin zaƙaƙuran ɗalibai masu hazaƙa.
Yace "Huɓɓasar da nake da ita akan harkar Ilimin musamman akan Ilimin mu na ƴaƴan talakawa ba aiki ba ne da zan gajiya da yaddar Allah, kamar yadda kuke gani, nima ban tsaya da karatuba saboda haka zan taimakamawa dukan wanda Allah ya bani ikon taimakamawa dai dai gwargwadon abinda zan iya."
"Taimakon da ake a ɓangarorin lafia, ci gaban ƙasa da al'umma zan faɗaɗa a Gidauniyarmu bada jimawaba da yaddar Allah."
"Babban burina shine Allah ya ci gaba da bani iko na zama sanadiyar samun sauƙin bayin Allah." Inji shi
Ya kara da cewa "Mu a Kano mun godewa Allah, akasarin yaranmu basu zaman banza, karatu ne ko sana'a wasuma duka, saboda haka ya zama wajibi muma mu bada gudunmuwa wajen ganin wannnan tarihi mai kyau ya ɗore a Kano." Ya jaddada
Idan dai za'a tuna ko a makon daya gabata, A.A Zaura ya ƙaddamar da wani shiri na samar da lafia ga kowa wato "Zaura Health For All" ZEL4ALL a turance a ƙarƙashin Gidauniyarsa ta A