14/08/2026
Gwamna Bala Ya Yabawa Jonathan da Obasanjo Bisa Halartar Taron Dimokuraɗiyya a Bauchi
Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ya mika godiyarsa da yabo ga tsoffin Shugabannin Ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan da Olusegun Obasanjo, bisa halartar taron Goodluck Jonathan Democracy Dialogue na shekarar 2026 da aka gudanar a Bauchi.
Gwamna Bala ya bayyana hakan ne yayin gudanar da taron cin abincin dare na girmama manyan baƙin. A jawabin sa, ya fayi iyakar ƙoƙarinsa wajen ayyana Jonathan a matsayin jagora da ke zama ginshiƙi kuma mai ba da shawara ga shugabanni da dama, yana mai cewa halayensa na jajircewa, hangen nesa, da tawali’u sun zama abin koyi a Afirka.
Kazalika, gwamnan ya mika godiyarsa ga tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Namadi Sambo, tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Iyorchia Ayu, da sarakunan gargajiya tare da sauran manyan baƙi da s**a girmama gayyatar.
A nasa ɓangaren, tsohon Shugaba Goodluck Jonathan ya nuna jin daɗinsa ga Gwamna Bala Mohammed da ɗaukacin gwamnatin Bauchi bisa kyakkyawar tarbar da aka yi musu. Ya kuma yabawa jihar kan abubuwan daftarin ci gaba da ta samu, musamman ta fannin bunƙasa ababen more rayuwa.
A ƙarshe, Jonathan ya jaddada buƙatar ƙarfafa ginshiƙan dimokuraɗiyya da shugabanci nagari, sannan ya mika godiya ga dukkanin mahalarta taron da s**a taru a Bauchi domin tattauna makomar dimokuraɗiyya a Najeriya da ma nahiyar Afirka baki ɗaya.
Inside Bauchi State
11-08-2026