11/11/2020
An zabi mutanen da zasu ci moriyar shirin a wannan daga jihohi goma da ke sassa daban-daban na Najeriya
A yayin da batagarin mutane ke tsaka da cigaba da barna a sassan kasa, gwamnatin tarayya ta sanar da kaddamar da shirin bunkasa tattalin arziki.
A karkashin wannan shiri, gwamnatin tarayya ta sanar da cewa ta fara biyan N30,000 ga masu sana'ar hannu.
A cewar gwamnatin tarayya, za ta biya kudin sau daya ga kowanne mutum.
Kudin da aka fara rabawa na daga cikin kudaden da aka ware domin farfado da kananan masana'antu da bullar annobar korona ta kassara.
An fara biyan kudaden ne zuwa asusun masu sana'ar hannu da aka tantance a jihohi goma.
Jihohi 10 da aka zaba a matsayin rukuni na farko domin fara biyan mutanensu sun hada da; Abuja, Lagos, Kaduna, Ondo, Kano, Borno, Abia, Bauchi, Anambra, Ribas, Filato, da Delta.
Mutanen da aka zaba daga jihohin sun aika bayanansu tsakanin 1 ga watan Oktoba zuwa ranar 10 ga wata ta shafin yanar gizo da aka bude domin neman tallafin.
Masu kananan sana'o'i
Source: Original
Shugaba Buhari ne ya kaddamar da shirin bawa kananan masana'antu tallafi (MSMEs Survival Fund) a cikin watan Maris, 2020.
Shirin ya na daga cikin babban tsarin raya tattalin arziki (NESP) wanda shugaba Buhari ya nada mataimakinsa, Farfesa Yemi Osinbajo, a matsayin jagora.
A saboda haka, ofishin Osinbajo ne zai sa ido a kan kaddamar da shirin tare da tafiyar da komai bisa manufofi da ka'idojin da gwamnati ta gindaya.
An tura masu yi wa jama'a rijistar zuwa sauran jihohin da za a bayar da tallafin a sauran rukunai da zasu biyo baya.
Gwamnati ta shawarci masu sana'o'in hannu su tuntubi shugabannin kungiyoyinsu domin mika sunayensu.
An fara rijistar mutane a rukuni na biyu daga ranar 19 ga watan Oktoba a jihohin Edo, Ogun, Ekiti, Katsina, Kebbi, Kogi, Kwara, Enugu, Ebonyi, Adamawa, Taraba, da Bayelsa.
A bangare guda, har yanzu ana cigaba da tantance bayanai da takardun wadanda s**a nemi tallafi a karkashin tsarin biya masu matsakaitan masana'antu.
Sai dai